• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Amsa Sunanta Na Aminiya Ta Kwarai Ga Kasashen Afrika

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Har kullum kulawar kasar Sin ga aminanta na Afrika, ya kasance abun burgewa, da ya kamata manyan kasashe irinta su yi koyi da shi. Yadda ake maganar an bar kasashen Afrika a baya idan ana tattauna a dandamalin duniya, kamata ya yi a rika ganin tallafin wadannan manyan kasashe a nahiyar ta Afrika idan har da gaske suke. Ban da kasar Sin, ba ka jin wata kasa dake abubuwan na tallafi masu kwari na a zo a gani, wadanda kuma suka shafi jama’a kai tsaye.

Hausawa kan ce ruwan da ya dake ka, shi ne ruwa. Tabbas haka ne, domin wanda ya ba ka tallafi na zahiri kuma ka amfana, hakika shi ne ya taimake ka kuma ya damu da kai.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

Yayin da tsarin kiwon lafiya ke fuskantar matsi a kasashen nahiyar, saboda tarin annoba da ake fama da su, kasar Sin ta yi hobbasa, inda a baya-bayan nan, ofishin jakadancinta dake Uganda da hadin gwiwar wasu kamfanonin kasar da ma tawagar jami’an lafiya dake kasar, suka mikawa asibitin sada zumunta na Sin da Uganda, kayayyakin aiki domin taimakawa kasar a yakin da take da cutar Ebola da kuma ta COVID-19.

Tun cikin 1983 kasar Sin ta fara tura jami’an lafiya da kayayyakin kiwon lafiya zuwa kasar Uganda, wanda kawo yanzu shekaru kusan 40 ke nan, amma ba ta gajiya ba. Wannan kadai ya isa ya kara tabbatarwa jama’ar duniya, musamman wadanda lamarin ya shafa kai tsaye cewa, kasar Sin ta kasance aminiya ta kwarai, kuma abun dagoro.

Baya ga tallafin kayayyakin, kasar Sin za ta taimaka wajen fadada asibitin zuwa cibiyar karbar marasa lafiya na gaggawa kamar haddura da makamantansu, wanda ake ganin ba kasar ce kadai za ta amfana ba, har ma da kasashe makwabta.

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Irin wannan tallafi da jama’a ke iya gani tare da amfana da shi kai tsaye, shi ne ke kara kaunar Sin a zukatan jama’ar Afrika, haka kuma ya sa take kara samun karbuwa a kasashensu.

Taimako ko agajin kiwon lafiya, muhimmin abu ne dake nuna cewa Sin ta damu da yanayin da al’ummar Afrika ke ciki, kuma da gaske aniyarta take, na ganin an samu al’umma mai kyakkyawar makoma. Hakika tallafin Sin bai tsaya a fatar baki ba, domin tana yi ana gani, kuma ana cin moriya. Ya kamata kasashe masu kiran kansu manya, su rage surutu, su yi koyi da kasar Sin wajen ganin al’ummar duniya sun samu ci gaba na bai daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba
Daga Birnin Sin

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Next Post
Sin Na Daukar Matakai Iri Daban-daban Don Farfado Da Tattalin Arziki Mai Dorewa

Sin Na Daukar Matakai Iri Daban-daban Don Farfado Da Tattalin Arziki Mai Dorewa

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.