• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Amsa Sunanta Na Aminiya Ta Kwarai Ga Kasashen Afrika

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Amsa Sunanta Na Aminiya Ta Kwarai Ga Kasashen Afrika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Har kullum kulawar kasar Sin ga aminanta na Afrika, ya kasance abun burgewa, da ya kamata manyan kasashe irinta su yi koyi da shi. Yadda ake maganar an bar kasashen Afrika a baya idan ana tattauna a dandamalin duniya, kamata ya yi a rika ganin tallafin wadannan manyan kasashe a nahiyar ta Afrika idan har da gaske suke. Ban da kasar Sin, ba ka jin wata kasa dake abubuwan na tallafi masu kwari na a zo a gani, wadanda kuma suka shafi jama’a kai tsaye.

Hausawa kan ce ruwan da ya dake ka, shi ne ruwa. Tabbas haka ne, domin wanda ya ba ka tallafi na zahiri kuma ka amfana, hakika shi ne ya taimake ka kuma ya damu da kai.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

Yayin da tsarin kiwon lafiya ke fuskantar matsi a kasashen nahiyar, saboda tarin annoba da ake fama da su, kasar Sin ta yi hobbasa, inda a baya-bayan nan, ofishin jakadancinta dake Uganda da hadin gwiwar wasu kamfanonin kasar da ma tawagar jami’an lafiya dake kasar, suka mikawa asibitin sada zumunta na Sin da Uganda, kayayyakin aiki domin taimakawa kasar a yakin da take da cutar Ebola da kuma ta COVID-19.

Tun cikin 1983 kasar Sin ta fara tura jami’an lafiya da kayayyakin kiwon lafiya zuwa kasar Uganda, wanda kawo yanzu shekaru kusan 40 ke nan, amma ba ta gajiya ba. Wannan kadai ya isa ya kara tabbatarwa jama’ar duniya, musamman wadanda lamarin ya shafa kai tsaye cewa, kasar Sin ta kasance aminiya ta kwarai, kuma abun dagoro.

Baya ga tallafin kayayyakin, kasar Sin za ta taimaka wajen fadada asibitin zuwa cibiyar karbar marasa lafiya na gaggawa kamar haddura da makamantansu, wanda ake ganin ba kasar ce kadai za ta amfana ba, har ma da kasashe makwabta.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Irin wannan tallafi da jama’a ke iya gani tare da amfana da shi kai tsaye, shi ne ke kara kaunar Sin a zukatan jama’ar Afrika, haka kuma ya sa take kara samun karbuwa a kasashensu.

Taimako ko agajin kiwon lafiya, muhimmin abu ne dake nuna cewa Sin ta damu da yanayin da al’ummar Afrika ke ciki, kuma da gaske aniyarta take, na ganin an samu al’umma mai kyakkyawar makoma. Hakika tallafin Sin bai tsaya a fatar baki ba, domin tana yi ana gani, kuma ana cin moriya. Ya kamata kasashe masu kiran kansu manya, su rage surutu, su yi koyi da kasar Sin wajen ganin al’ummar duniya sun samu ci gaba na bai daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Next Post

Sin Na Daukar Matakai Iri Daban-daban Don Farfado Da Tattalin Arziki Mai Dorewa

Related

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

10 hours ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

11 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

12 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

14 hours ago
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

15 hours ago
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

1 day ago
Next Post
Sin Na Daukar Matakai Iri Daban-daban Don Farfado Da Tattalin Arziki Mai Dorewa

Sin Na Daukar Matakai Iri Daban-daban Don Farfado Da Tattalin Arziki Mai Dorewa

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.