ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Amsa Sunanta Na Aminiya Ta Kwarai Ga Kasashen Afrika

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Har kullum kulawar kasar Sin ga aminanta na Afrika, ya kasance abun burgewa, da ya kamata manyan kasashe irinta su yi koyi da shi. Yadda ake maganar an bar kasashen Afrika a baya idan ana tattauna a dandamalin duniya, kamata ya yi a rika ganin tallafin wadannan manyan kasashe a nahiyar ta Afrika idan har da gaske suke. Ban da kasar Sin, ba ka jin wata kasa dake abubuwan na tallafi masu kwari na a zo a gani, wadanda kuma suka shafi jama’a kai tsaye.

Hausawa kan ce ruwan da ya dake ka, shi ne ruwa. Tabbas haka ne, domin wanda ya ba ka tallafi na zahiri kuma ka amfana, hakika shi ne ya taimake ka kuma ya damu da kai.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

Yayin da tsarin kiwon lafiya ke fuskantar matsi a kasashen nahiyar, saboda tarin annoba da ake fama da su, kasar Sin ta yi hobbasa, inda a baya-bayan nan, ofishin jakadancinta dake Uganda da hadin gwiwar wasu kamfanonin kasar da ma tawagar jami’an lafiya dake kasar, suka mikawa asibitin sada zumunta na Sin da Uganda, kayayyakin aiki domin taimakawa kasar a yakin da take da cutar Ebola da kuma ta COVID-19.

ADVERTISEMENT

Tun cikin 1983 kasar Sin ta fara tura jami’an lafiya da kayayyakin kiwon lafiya zuwa kasar Uganda, wanda kawo yanzu shekaru kusan 40 ke nan, amma ba ta gajiya ba. Wannan kadai ya isa ya kara tabbatarwa jama’ar duniya, musamman wadanda lamarin ya shafa kai tsaye cewa, kasar Sin ta kasance aminiya ta kwarai, kuma abun dagoro.

Baya ga tallafin kayayyakin, kasar Sin za ta taimaka wajen fadada asibitin zuwa cibiyar karbar marasa lafiya na gaggawa kamar haddura da makamantansu, wanda ake ganin ba kasar ce kadai za ta amfana ba, har ma da kasashe makwabta.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Irin wannan tallafi da jama’a ke iya gani tare da amfana da shi kai tsaye, shi ne ke kara kaunar Sin a zukatan jama’ar Afrika, haka kuma ya sa take kara samun karbuwa a kasashensu.

Taimako ko agajin kiwon lafiya, muhimmin abu ne dake nuna cewa Sin ta damu da yanayin da al’ummar Afrika ke ciki, kuma da gaske aniyarta take, na ganin an samu al’umma mai kyakkyawar makoma. Hakika tallafin Sin bai tsaya a fatar baki ba, domin tana yi ana gani, kuma ana cin moriya. Ya kamata kasashe masu kiran kansu manya, su rage surutu, su yi koyi da kasar Sin wajen ganin al’ummar duniya sun samu ci gaba na bai daya.

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Sin Na Daukar Matakai Iri Daban-daban Don Farfado Da Tattalin Arziki Mai Dorewa

Sin Na Daukar Matakai Iri Daban-daban Don Farfado Da Tattalin Arziki Mai Dorewa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.