• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasan Karshe: Tarihi Da Yadda Za’a Kece Raini A Qatar

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Wasan Karshe: Tarihi Da Yadda Za’a Kece Raini A Qatar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Argentina za ta fafata da Faransa a wasan karshe na Gasar Cin Kofin Duniya ranar Lahadi da Qatar ke karbar bakunci.

Tambayar da kowa yake yi shine ko dan wasa Messi zai dauki Kofin Duniya na farko a tarihin rayuwar sa, ko kuwa Mbappe zai lashe na biyu a jere a karawar da za su buga da misalin karfe 4 a filin wasa na Lusail.

  • ‘Yan Wasan Da Suka Fi Zura Kwallaye A Gasar Kofin Duniya Ta Qatar Zuwa Yanzu

Messi, wanda yake buga wasa a PSG mai shekara 35, ya lashe gasar Ballon d’Or bakwai da Copa America da sauran kofuna da yawa, amma bai taba daukar na Duniya ba.

Argentina ta lashe Kofin Duniya biyu jumulla, amma rabon ta da lashe kofin tun 1986 karkashin jagorancin marigayi Diego Maradona.

Wannan karawar za’a yi tsakanin ‘yan kwallon Paris St Germain da suke buga wasa tare, wato Messi da Kylian Mbappe.

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

‘Yan wasan biyu na takarar lashe kyautar takalmin zinare a matakin, wanda ke kan gaba a cin kwallaye a Gasar, kowanne yana da biyar-biyar a raga a Qatar.

Yayin da Olivier Giroud na Fransa da dan kwallon Argentina, Julian Alvarez kowanne yana da hur-hudu a raga.

Messi ya ja ragamar Argentina kai wa wasan karshe a Gasar Kofin Duniya a 2014, amma Jamus ta doke su 1-0 a Brazil, bayan karin lokaci, Mario Gotze ne ya ci kwallon.

A tarihi Argentina ta lashe kofin Duniya guda biyu na farko a gida a 1978, sannan a 1986 a kasar Mexico.

Faransa ma guda biyu ne da ita, wadda ta fara dauka a gida a 1998, sannan ta lashe a 2018 a Rasha.

Kowacce na fatan daukar na uku jumulla, sai dai Fransa na sa ran daukar na biyu a jere bayan bajintar da Brazil ta yi a 1962 – sai dai Italiya ce ta kafa tarihin cin biyu a jere a 1934 da kuma a 1938.

Kasashen biyu sun kece raini sau uku a Gasar Kofin Duniya, inda Argentina ta yi nasara a fafatawar cikin rukuni a 1930 da kuma 1978 – sai dai Faransa ce ta ci Argentina 4-3 a zagayen siri daya kwale a 2018.

Argentina za ta buga wasan karshe na shida a Gasar Kofin Duniya, Jamus ce kan gaba a yawan kai wa fafatawar karshe inda ta buga guda takwas.

Argentina ta dauki Kofin a 1978 da 1986, sannan aka doke ta a karawar karshe a 1930 da 1990 da kuma 2014.

Watakila Argentina ta zama ta biyu da ta yi rashin nasara a wasan farko a Kofin Duniya, sannan ta lashe Gasar kamar yadda Sifaniya ta yi a 2010.

Haka kuma kila Messi ya zama na uku daga Argentina da zai lashe takalmin zinare, bayan Guillermo Stabile a 1930 da kuma Mario Kempes a 1978.

Faransa ta halarci karawar karshe a Gasar Kofin Duniya karo na hudu.

Faransa na fatan zama ta uku da za ta lashe Kofin Duniya biyu a jere, bayan Italiya a 1934 da 1938 da kuma Brazil 1958 da 1962.

‘Yan Wasan Faransa Basu da lafiya

Yan wasan Faransa da dama sun kamu da sanyi a sansaninsu da ke Doha gabanin wasan na karshe.

Na baya bayannan sune masu tsaron baya Raphael Varane da Ibrahim Kounate, wadanda rashin lafiyar ta hana su yin atisaye.

Dama mai tsaron baya Dayot Upamecano da dan wasan tsakiya Adrien Rabiot ba su samu buga wasan kusa da karshe ba da Faransa ta yi nasara kan Maroko.

Kasar Qatar ta kafa tarihi

Kamar yadda shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, Gianni Infantino ya bayyana, Qatar ta yi nasarar shirya gasar cin kofin duniya da tarihi ba zai taba mantawa da ita ba.

A cewar sa, duka kasashen da suka samu halartar gasar sun bar Qatar da ke Gabas ta Tsakiya da wani abun alkhairi da ba zasu taba mantawa ba.

To amma babban abunda yafi jan hankali a hirar da ya yi da manema labarai shi ne, batun sauya gasar kofin duniya daga kasashe 32 zuwa 48.

Kuma za’a fara aiwatar da hakan ne a gasar ta gaba, ta hadaka tsakanin kasashen Amurka da Canada da kuma Mexico a 2026.

Ana tunanin samar da rukuni 16 mai kasashe uku-uku, ko kuma rukuni 12 mai kasashe hudu-hudu.

A karkashin sabon tsarin nahiyoyi za su samu karin kason kasashen da za su wakilce su, inda ake hasashen Afrika za ta samu karin kasashe daga biyar zuwa tara.

Za kuma a fadada gasar kungiyoyin duniya 32, da zasu buga tsakaninsu a gasar da ya kira FIFA Club World Cup ta maza da ta mata.

A gasar France 98 ce FIFA ta fadada gasar kofin duniya zuwa 32.

Wanene alkalin wasan da zai jagoranci wasan na karshe?

Tuni dai kwamitin da ke jagorancin alkalan hukumar kwallon kafa ta duniya, ya zabi Szymon Marciniak a matsayin wanda zai jagoranci wasan na karshe tsakanin Faransa da Argentina.

Marciniak, dan kasar Poland mai shekaru 41 a duniya na cikin tawagar alkalan da suka jagorancin wasannin kasashen biyu kafin a kawo wannan mataki na wasan karshe.

Akwai wasan da Argentina ta doke Australia a zagayen kwaf daya, da kuma wanda Faransa ta doke Denmark a wasan rukuni duka shine ya jagoranci wasannin.

A ranar Alhamis ne FIFA ta sanar da sunansa a matsayin wanda zai raba gardama, a wasan da duniya ke dakon gani tuntuni.

Ana yi wa Szymon Marciniak kallon alkalin wasa mafi shahara a Poland da ma daukacin Turai, kuma kwarewarsa tasa hukumar kwallon kafar Turai ta bashi alkalancin wasan karshe na Uefa Super Cup.

Kazalika FIFA ta bayyana sunayen Pawel Sokolnicki da Tomasz Listkiewicz, wadanda dukansu suma yan Poland ne, a matsayin masu taimaka masa.

A al’ada a kan bai wa tawagar masu alkalanci zinariya kafin bada kofi ga kasar da ta yi nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Tare Da Gano Bindigar AK47 A Kebbi

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Banka Wa Wata Babbar Kotu Wuta A Jihar Imo

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

2 days ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

5 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

5 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

7 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

7 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

1 week ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Banka Wa Wata Babbar Kotu Wuta A Jihar Imo

'Yan Bindiga Sun Banka Wa Wata Babbar Kotu Wuta A Jihar Imo

LABARAI MASU NASABA

Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.