ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasan Karshe: Tarihi Da Yadda Za’a Kece Raini A Qatar

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Qatar

A yau Argentina za ta fafata da Faransa a wasan karshe na Gasar Cin Kofin Duniya ranar Lahadi da Qatar ke karbar bakunci.

Tambayar da kowa yake yi shine ko dan wasa Messi zai dauki Kofin Duniya na farko a tarihin rayuwar sa, ko kuwa Mbappe zai lashe na biyu a jere a karawar da za su buga da misalin karfe 4 a filin wasa na Lusail.

  • ‘Yan Wasan Da Suka Fi Zura Kwallaye A Gasar Kofin Duniya Ta Qatar Zuwa Yanzu

Messi, wanda yake buga wasa a PSG mai shekara 35, ya lashe gasar Ballon d’Or bakwai da Copa America da sauran kofuna da yawa, amma bai taba daukar na Duniya ba.

ADVERTISEMENT

Argentina ta lashe Kofin Duniya biyu jumulla, amma rabon ta da lashe kofin tun 1986 karkashin jagorancin marigayi Diego Maradona.

Wannan karawar za’a yi tsakanin ‘yan kwallon Paris St Germain da suke buga wasa tare, wato Messi da Kylian Mbappe.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

‘Yan wasan biyu na takarar lashe kyautar takalmin zinare a matakin, wanda ke kan gaba a cin kwallaye a Gasar, kowanne yana da biyar-biyar a raga a Qatar.

Yayin da Olivier Giroud na Fransa da dan kwallon Argentina, Julian Alvarez kowanne yana da hur-hudu a raga.

Messi ya ja ragamar Argentina kai wa wasan karshe a Gasar Kofin Duniya a 2014, amma Jamus ta doke su 1-0 a Brazil, bayan karin lokaci, Mario Gotze ne ya ci kwallon.

A tarihi Argentina ta lashe kofin Duniya guda biyu na farko a gida a 1978, sannan a 1986 a kasar Mexico.

Faransa ma guda biyu ne da ita, wadda ta fara dauka a gida a 1998, sannan ta lashe a 2018 a Rasha.

Kowacce na fatan daukar na uku jumulla, sai dai Fransa na sa ran daukar na biyu a jere bayan bajintar da Brazil ta yi a 1962 – sai dai Italiya ce ta kafa tarihin cin biyu a jere a 1934 da kuma a 1938.

Kasashen biyu sun kece raini sau uku a Gasar Kofin Duniya, inda Argentina ta yi nasara a fafatawar cikin rukuni a 1930 da kuma 1978 – sai dai Faransa ce ta ci Argentina 4-3 a zagayen siri daya kwale a 2018.

Argentina za ta buga wasan karshe na shida a Gasar Kofin Duniya, Jamus ce kan gaba a yawan kai wa fafatawar karshe inda ta buga guda takwas.

Argentina ta dauki Kofin a 1978 da 1986, sannan aka doke ta a karawar karshe a 1930 da 1990 da kuma 2014.

Watakila Argentina ta zama ta biyu da ta yi rashin nasara a wasan farko a Kofin Duniya, sannan ta lashe Gasar kamar yadda Sifaniya ta yi a 2010.

Haka kuma kila Messi ya zama na uku daga Argentina da zai lashe takalmin zinare, bayan Guillermo Stabile a 1930 da kuma Mario Kempes a 1978.

Faransa ta halarci karawar karshe a Gasar Kofin Duniya karo na hudu.

Faransa na fatan zama ta uku da za ta lashe Kofin Duniya biyu a jere, bayan Italiya a 1934 da 1938 da kuma Brazil 1958 da 1962.

‘Yan Wasan Faransa Basu da lafiya

Yan wasan Faransa da dama sun kamu da sanyi a sansaninsu da ke Doha gabanin wasan na karshe.

Na baya bayannan sune masu tsaron baya Raphael Varane da Ibrahim Kounate, wadanda rashin lafiyar ta hana su yin atisaye.

Dama mai tsaron baya Dayot Upamecano da dan wasan tsakiya Adrien Rabiot ba su samu buga wasan kusa da karshe ba da Faransa ta yi nasara kan Maroko.

Kasar Qatar ta kafa tarihi

Kamar yadda shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, Gianni Infantino ya bayyana, Qatar ta yi nasarar shirya gasar cin kofin duniya da tarihi ba zai taba mantawa da ita ba.

A cewar sa, duka kasashen da suka samu halartar gasar sun bar Qatar da ke Gabas ta Tsakiya da wani abun alkhairi da ba zasu taba mantawa ba.

To amma babban abunda yafi jan hankali a hirar da ya yi da manema labarai shi ne, batun sauya gasar kofin duniya daga kasashe 32 zuwa 48.

Kuma za’a fara aiwatar da hakan ne a gasar ta gaba, ta hadaka tsakanin kasashen Amurka da Canada da kuma Mexico a 2026.

Ana tunanin samar da rukuni 16 mai kasashe uku-uku, ko kuma rukuni 12 mai kasashe hudu-hudu.

A karkashin sabon tsarin nahiyoyi za su samu karin kason kasashen da za su wakilce su, inda ake hasashen Afrika za ta samu karin kasashe daga biyar zuwa tara.

Za kuma a fadada gasar kungiyoyin duniya 32, da zasu buga tsakaninsu a gasar da ya kira FIFA Club World Cup ta maza da ta mata.

A gasar France 98 ce FIFA ta fadada gasar kofin duniya zuwa 32.

Wanene alkalin wasan da zai jagoranci wasan na karshe?

Tuni dai kwamitin da ke jagorancin alkalan hukumar kwallon kafa ta duniya, ya zabi Szymon Marciniak a matsayin wanda zai jagoranci wasan na karshe tsakanin Faransa da Argentina.

Marciniak, dan kasar Poland mai shekaru 41 a duniya na cikin tawagar alkalan da suka jagorancin wasannin kasashen biyu kafin a kawo wannan mataki na wasan karshe.

Akwai wasan da Argentina ta doke Australia a zagayen kwaf daya, da kuma wanda Faransa ta doke Denmark a wasan rukuni duka shine ya jagoranci wasannin.

A ranar Alhamis ne FIFA ta sanar da sunansa a matsayin wanda zai raba gardama, a wasan da duniya ke dakon gani tuntuni.

Ana yi wa Szymon Marciniak kallon alkalin wasa mafi shahara a Poland da ma daukacin Turai, kuma kwarewarsa tasa hukumar kwallon kafar Turai ta bashi alkalancin wasan karshe na Uefa Super Cup.

Kazalika FIFA ta bayyana sunayen Pawel Sokolnicki da Tomasz Listkiewicz, wadanda dukansu suma yan Poland ne, a matsayin masu taimaka masa.

A al’ada a kan bai wa tawagar masu alkalanci zinariya kafin bada kofi ga kasar da ta yi nasara.

Qatar
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Banka Wa Wata Babbar Kotu Wuta A Jihar Imo

'Yan Bindiga Sun Banka Wa Wata Babbar Kotu Wuta A Jihar Imo

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.