• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dandazon ‘Yan PDP Da APC Sun Sauya Sheka Zuwa NNPP A Gombe

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
Dandazon ‘Yan PDP Da APC Sun Sauya Sheka Zuwa NNPP A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar gwamnan Jihar Gombe a jam’iyyar NNPP, Khamisu Ahmed Mailantarki, ya na ci gaba da karɓar dandazon manya da ƙananan magoya bayan APC mai mulkin jihar da kuma PDP.

 

A ƙarshen makon nan ne Mailantarki ya haska wa wasu manyan mambobin PDP hanya, su ka bi ta gwadaben da su ka koma NNPP.

  • ‘Yan Daba Sun Raunata Mutum 17 Cikin Tawagar Dan Takarar Sanatan APC A Kano

Mambobin dai zaratan magoya bayan fitaccen ɗan siyasar nan ne Jamil Isyaku Gwamna, waɗanda ake kiran ƙungiyar su da suna Sardauna Dawo-Dawo.

 

Labarai Masu Nasaba

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

A ranar Juma’a ce Mailantarki ya karɓi dandazon ‘yan PDP ɗin a bisa tarbar su da Shugaban NNPP na Jihar Gombe ya yi, wato Alhaji Abdulahi Maikano.

 

Wannan dandazon magoya baya dai sun canja sunan su daga Sardauna Dawo-Dawo zuwa Mailantarki Movement, bayan sauya sheƙar su daga PDP zuwa NNPP.

 

Sun bayyana cewa sun yanke shawarar goyon bayan ɗan takarar da “matashi ne mai jini a jika, wanda ke da jama’a a kowane ɓangaren al’umma, nagari na kowa, ƙwararre, kuma mai zuciyar tausayin al’umma.”

 

Shugaban tawagar mai suna Muhammad Makson ya bayyana cewa Gombawa ba su da wata matsala da Mailantarki, domin an jaraba shi a baya, kuma ya ci jarabawar riƙon amanar da aka damƙa masa.

 

“A kan haka, Mailantarki na da gogewar da zai iya magancewa da shawo kan matsalolin da su ka dabaibaye jihar Gombe.

 

“Gaba ɗayan mu ne mu ka yi shawarar ficewa daga PDP mu ka yanke shawarar dawowa cikin NNPP, saboda buƙatar ganin mun samu nagartaccen shugabancin da ya fi dacewa da Jihar Gombe.

 

“Mun yi amanna cewa Mailantarki ne zai iya tsamo Jihar Gombe daga kwazazzabon ramin da APC ta jefa jihar, sakamakon tuƙin gangancin da ake yi da motar da APC ta cika da lodin al’ummar Gombe.”

 

Makson ya ce waɗanda su ka fice daga PDP ɗin zuwa NNPP akwai shugabanni 2000, mambobi sama da 20,000 a faɗin mazaɓu 114 na Jihar Gombe.

 

Mailantarki ya tabbatar masu da cewa shi da NNPP za su tafi tare da su domin a gudu tare, a yi nasarar kafa gwamnati tare.

 

Daga nan ya roƙesu cewa sai sun ƙara tashi tsaye sosai wajen yaɗa manufofin NNPP da tallata ‘yan takarar jam’iyyar a cikin yankunan karkara, ta yadda za a kawar da gwamnatin APC a ranar zaɓen 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Daba Sun Raunata Mutum 17 Cikin Tawagar Dan Takarar Sanatan APC A Kano

Next Post

Tsokaci A Kan Karin Aure Cikin Sirri (II)

Related

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

9 hours ago
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci
Siyasa

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

1 day ago
Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

3 days ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

3 days ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

5 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

6 days ago
Next Post
Tsokaci A Kan Karin Aure Cikin Sirri (II)

Tsokaci A Kan Karin Aure Cikin Sirri (II)

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.