• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Amurka ta sanar da janye jiki daga kasar Syria tun shekaru 4 da suka wuce, amma har zuwa yanzu, wasu sojojin kasar Amurka 900 na ci gaba da kasancewa a arewacin kasar.

A cewar kasar Amurka, dalilin da ya sa hakan shi ne magance farfadowar kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi a Syria. Amma a cewar gwamnatin kasar Syria, wadannan sojoji na kasar Amurka na kwatan danyen mai, da alkama, da sauran albarkatu iri-iri na kasar.

  • Bai Kamata Amurka Ta Kara Fadawa Hanyar Da Ba Ta Dace Ba

Hakika wani babban aiki na wadannan sojojin kasar Amurka, shi ne samar da goyon baya ga dakarun kasar Syria masu kin jinin gwamnati, inda ake ba su taimako wajen mallakar mahakan mai da iskar gas dake arewa maso gabashin kasar, da jigilar mai zuwa kasar Iraki domin sayar da shi.

A cewar gwamnatin kasar Syria, sojojin Amurka da dakaru masu kin jinin gwamnati, sun riga sun haddasa mata asarar da ta kai dalar Amukra biliyan 25.9. Kana a watanni 6 na farko na shekarar bana, sojojin Amurka da dakarun da suke samun goyon baya daga wajensu, sun kwaci fiye da kaso 80 na danyen man da aka haka a kasar Syria.

Ban da wannan kuma, kasar Amurka da wasu kawayenta na ci gaba da saka takunkumi kan kasar Syria, ko da yake kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya bai samar da iznin yin haka ba. Wannan takunkumi ya shafi bangarorin tattalin arzikin kasar Syira masu muhimmanci, da suka hada da danyen mai, da wutar lantarki, da cinikayya, da dai sauransu, lamarin da ya haddasa raguwar kudin shigar da jama’ar kasar suke samu, da hauhawar farashin kaya.

Labarai Masu Nasaba

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Zuwa yanzu kashi 90% na al’ummar kasar sun tsunduma cikin kangin talauci. Kana daga shekarar 2019 har zuwa yanzu, matsakaicin farashin kayayyaki na kasar ya karu da kashi 800%. Kuma wani abun takaici shi ne, Amurka da kawayenta sun ce dalilin da ya sa suka kakaba wa kasar Syria takunkumi shi ne kare jama’ar kasar.

Hakika Amurka ba za ta daina yin tasiri a kasar Syria ba. Ta hanyar raunana gwamnatin Syria da takunkumi, da taimakawa dakaru masu kin jinin gwamnati da damar shawo kan albarkatun danyen mai da iskar gas, kasar Amurka na ci gaba da kokarin neman hambarar da gwamnatin kasar. Ko da yake tana gudanar da ayyukan fakewa da kalmomin “dimokuradiya”, da “hakkin dan Adam”, da “tsaro”, da “zaman lafiya”. Amma kar mu manta, cikin shekaru 20 da suka wuce, matakan da kasar Amurka ta dauka a kasashe da yankuna 85, sun haddasa asarar rayukan mutane kimanin dubu 900, da rashin matsugunan mutane fiye da miliyan 38.

Tutocin “Dimokuradiyya”, da “Hakkin dan Adam” da kasar Amurka ta rike sun riga sun lallata sosai. Anya kasar za ta iya ci gaba da fakewa da su? (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan AS’HABUL KAHFI Za Su Daukaka Kara Kan Hukuncin Kisa Ga Abduljabbar

Next Post

Masu Garkuwa Sun Kashe ‘Yan Gida Ɗaya Bayan Sun Karɓi Kudin Fansarsu Naira Miliyan 60

Related

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

2 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

4 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

5 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

16 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

20 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

21 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Yara 3, Sun Bukaci Kudin Fansa Naira Miliyan 100 A Jihar Kogi

Masu Garkuwa Sun Kashe 'Yan Gida Ɗaya Bayan Sun Karɓi Kudin Fansarsu Naira Miliyan 60

LABARAI MASU NASABA

Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.