ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Amurka ta sanar da janye jiki daga kasar Syria tun shekaru 4 da suka wuce, amma har zuwa yanzu, wasu sojojin kasar Amurka 900 na ci gaba da kasancewa a arewacin kasar.

A cewar kasar Amurka, dalilin da ya sa hakan shi ne magance farfadowar kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi a Syria. Amma a cewar gwamnatin kasar Syria, wadannan sojoji na kasar Amurka na kwatan danyen mai, da alkama, da sauran albarkatu iri-iri na kasar.

  • Bai Kamata Amurka Ta Kara Fadawa Hanyar Da Ba Ta Dace Ba

Hakika wani babban aiki na wadannan sojojin kasar Amurka, shi ne samar da goyon baya ga dakarun kasar Syria masu kin jinin gwamnati, inda ake ba su taimako wajen mallakar mahakan mai da iskar gas dake arewa maso gabashin kasar, da jigilar mai zuwa kasar Iraki domin sayar da shi.

ADVERTISEMENT

A cewar gwamnatin kasar Syria, sojojin Amurka da dakaru masu kin jinin gwamnati, sun riga sun haddasa mata asarar da ta kai dalar Amukra biliyan 25.9. Kana a watanni 6 na farko na shekarar bana, sojojin Amurka da dakarun da suke samun goyon baya daga wajensu, sun kwaci fiye da kaso 80 na danyen man da aka haka a kasar Syria.

Ban da wannan kuma, kasar Amurka da wasu kawayenta na ci gaba da saka takunkumi kan kasar Syria, ko da yake kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya bai samar da iznin yin haka ba. Wannan takunkumi ya shafi bangarorin tattalin arzikin kasar Syira masu muhimmanci, da suka hada da danyen mai, da wutar lantarki, da cinikayya, da dai sauransu, lamarin da ya haddasa raguwar kudin shigar da jama’ar kasar suke samu, da hauhawar farashin kaya.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Zuwa yanzu kashi 90% na al’ummar kasar sun tsunduma cikin kangin talauci. Kana daga shekarar 2019 har zuwa yanzu, matsakaicin farashin kayayyaki na kasar ya karu da kashi 800%. Kuma wani abun takaici shi ne, Amurka da kawayenta sun ce dalilin da ya sa suka kakaba wa kasar Syria takunkumi shi ne kare jama’ar kasar.

Hakika Amurka ba za ta daina yin tasiri a kasar Syria ba. Ta hanyar raunana gwamnatin Syria da takunkumi, da taimakawa dakaru masu kin jinin gwamnati da damar shawo kan albarkatun danyen mai da iskar gas, kasar Amurka na ci gaba da kokarin neman hambarar da gwamnatin kasar. Ko da yake tana gudanar da ayyukan fakewa da kalmomin “dimokuradiya”, da “hakkin dan Adam”, da “tsaro”, da “zaman lafiya”. Amma kar mu manta, cikin shekaru 20 da suka wuce, matakan da kasar Amurka ta dauka a kasashe da yankuna 85, sun haddasa asarar rayukan mutane kimanin dubu 900, da rashin matsugunan mutane fiye da miliyan 38.

Tutocin “Dimokuradiyya”, da “Hakkin dan Adam” da kasar Amurka ta rike sun riga sun lallata sosai. Anya kasar za ta iya ci gaba da fakewa da su? (Bello Wang)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Yara 3, Sun Bukaci Kudin Fansa Naira Miliyan 100 A Jihar Kogi

Masu Garkuwa Sun Kashe 'Yan Gida Ɗaya Bayan Sun Karɓi Kudin Fansarsu Naira Miliyan 60

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.