• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DA DUMI-DUMI: An Sace Mutum 16 A Wani Sabon Hari Da Aka Kai Jihar Kaduna

by Muhammad
3 years ago
Da

A wani sabon hari da ‘Yan bindiga suka kai sun sace mutane 16 a unguwar Angwan Pa da ke karamar hukumar Kajuru ta jihar Kaduna.

Wani mazaunin yankin wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce maharan sun afkawa yankin a ranar Litinin da misalin karfe 7:30 na dare, sa’o’i 24 bayan harin ranar Kirsimeti da aka kai Angwan Aku, da ke karamar hukumar Kajuru, inda aka kashe mutum 1 tare da jikkata wasu da sace mutum 45.

  • Wani Shahararren Dan Bindiga Ya Shiga Hannun ‘Yansanda A Jihar Kaduna
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 37 Tare Da Kone Gidaje Sama Da 100 A Garin Kaura, Kaduna

Mazaunin yankin wanda ya bukacu a sakaya sunansa, ya ce ‘yan bindigar sun mamaye yankin ne da misalin karfe 7:30 na dare inda suka kewaye kauyen, suka yi ta yin harbe-harbe.

Ya ce yayin kai harin sun yi awon gaba da mutane 53 amma 37 daga cikinsu sun tsere inda suka koma gida a safiyar ranar Talata, inda suka yi garkuwa da 16.

A cewarsa, kananan kauyukan da ba su da yawa a yanzu ‘yan bindigar ne ke kai hari, yana mai jaddada cewa: “Ba mu yi tsammanin ‘yan bindigar za su kai wa Anguwan Pa hari ba, domin bayan harin da aka kai wa Anguwan Aku a ranar Lahadin da ta gabata, an tura sojoji domin kwantar da tarzoma a yankin.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

“’Yan bindigar sun zo ne da misalin karfe 7:30 na yammacin jiya ramar Litinin inda suka kewaye kauyen. Yawancin lokaci suna zuwa da yawa sosai dauke da makamai.

“Za su shiga cikin yankin kawai, kafin ku ankara, sun riga sun kewaye ko’ina.

“Idan ka gudu za su harbe ka su kashe ka. Ba su saba shiga manyan yankuna da ke da yawan jama’a ba.

“Suna kai hari kananan kauyukan da ba su da mutane da yawa. Ba sa kuskura su shiga manyan kauyuka domin su ma suna tsoron asarar rayukansu.

“Yawancin mutanen karkara a Kajuru suna rayuwa ne cikin tsoro da fargaba.” A cewarsa.

An tuntubi, Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kaduna, DSP Muhammad Jalige, don jin halin da ake ciki kan sabon harin sai dai bamu samu amsa ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Next Post
Ana Gab Da Kammala Ginin Hedkwatar Africa CDC Da Sin Ta Dauki Nauyinsa

Dangantakar Sin Da Afrika Ta Kai Wani Mataki Da Babu Wanda Zai Iya Lalatawa

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.