ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DA DUMI-DUMI: An Sace Mutum 16 A Wani Sabon Hari Da Aka Kai Jihar Kaduna

by Muhammad
4 years ago
Da

A wani sabon hari da ‘Yan bindiga suka kai sun sace mutane 16 a unguwar Angwan Pa da ke karamar hukumar Kajuru ta jihar Kaduna.

Wani mazaunin yankin wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce maharan sun afkawa yankin a ranar Litinin da misalin karfe 7:30 na dare, sa’o’i 24 bayan harin ranar Kirsimeti da aka kai Angwan Aku, da ke karamar hukumar Kajuru, inda aka kashe mutum 1 tare da jikkata wasu da sace mutum 45.

  • Wani Shahararren Dan Bindiga Ya Shiga Hannun ‘Yansanda A Jihar Kaduna
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 37 Tare Da Kone Gidaje Sama Da 100 A Garin Kaura, Kaduna

Mazaunin yankin wanda ya bukacu a sakaya sunansa, ya ce ‘yan bindigar sun mamaye yankin ne da misalin karfe 7:30 na dare inda suka kewaye kauyen, suka yi ta yin harbe-harbe.

ADVERTISEMENT

Ya ce yayin kai harin sun yi awon gaba da mutane 53 amma 37 daga cikinsu sun tsere inda suka koma gida a safiyar ranar Talata, inda suka yi garkuwa da 16.

A cewarsa, kananan kauyukan da ba su da yawa a yanzu ‘yan bindigar ne ke kai hari, yana mai jaddada cewa: “Ba mu yi tsammanin ‘yan bindigar za su kai wa Anguwan Pa hari ba, domin bayan harin da aka kai wa Anguwan Aku a ranar Lahadin da ta gabata, an tura sojoji domin kwantar da tarzoma a yankin.

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

“’Yan bindigar sun zo ne da misalin karfe 7:30 na yammacin jiya ramar Litinin inda suka kewaye kauyen. Yawancin lokaci suna zuwa da yawa sosai dauke da makamai.

“Za su shiga cikin yankin kawai, kafin ku ankara, sun riga sun kewaye ko’ina.

“Idan ka gudu za su harbe ka su kashe ka. Ba su saba shiga manyan yankuna da ke da yawan jama’a ba.

“Suna kai hari kananan kauyukan da ba su da mutane da yawa. Ba sa kuskura su shiga manyan kauyuka domin su ma suna tsoron asarar rayukansu.

“Yawancin mutanen karkara a Kajuru suna rayuwa ne cikin tsoro da fargaba.” A cewarsa.

An tuntubi, Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Kaduna, DSP Muhammad Jalige, don jin halin da ake ciki kan sabon harin sai dai bamu samu amsa ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Da
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Tsohon Minista Uche Nnaji Kan Zargin Amfani Da Takardun Bogi

July 1, 2026
Next Post
Ana Gab Da Kammala Ginin Hedkwatar Africa CDC Da Sin Ta Dauki Nauyinsa

Dangantakar Sin Da Afrika Ta Kai Wani Mataki Da Babu Wanda Zai Iya Lalatawa

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.