• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Albishir Ga ’Yan Kasuwar Ketare Dake Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Albishir Ga ’Yan Kasuwar Ketare Dake Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun lokacin da kasar Sin ta sanar da inganta matakanta na yaki da annobar COVID-19, kanana da manyan harkoki na kasuwanci ke kara bunkasa a sassa daban-daban na fadin kasar. Tituna sun kara cika da ababan hawa, wuraren shakatawa da na motsa jiki ma ba a bar su a baya ba.

Ana haka ne kuma, sai hukumomi suka sanar da kaddamar da sauyi a dokar gudanar da rijistar hada-hadar cinikayyar kamfanonin ketare dake cikin kasar, duk da nufin kara bunkasa harkokin kasuwanci a kasar.

  • Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Na Shugaban CMG 

A karkashin wannan sauyi, hukumomin da abun ya shafa, sun dakatar da neman takardun rajistar kasuwancin waje, daga kamfanonin dake hada hadar shige da ficen hajoji, da takardun shaidar rajistar fasaha ta kwangilolin shige da fice, da shaidar kayyade hajoji, da takardun shaidar gudanar da kasuwanci na gwamnati, da ma wasu sauran takardu masu nasaba da hakan. Matakin dake kara tabbatar da alkawarin kasar na kara zurfafa bude kofa.

Ma’aikatar cinikayyar kasar Sin a nata bangare, ta ce wannan sauyi na da matukar muhimmanci ga masu gudanar da harkokin kasuwancin waje dake kasar Sin. Kaza lika sabon salo ne da gwamnatin Sin ta bullo da shi domin bunkasa cinikayya, da sakarwa kasuwa mara.

Masu fashin baki na cewa, matakin zai taimaka wajen kyautata damar gudanar da kasuwanci a saukake, da ingiza damar bunkasa cinikayyar kamfanonin waje, da bunkasa cinikayya mai nagarta, da kara bude kofa bisa matsayin koli.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Wani rahoton bincike ya nuna cewa, a cikin ’yan shekarun nan, manyan kamfanonin kera kayayyaki na kasar Sin, sun samu ci gaba matuka, inda kasuwar ta kara samun darajar da ma fadada tasirinta a kasuwannin ketare.

A halin da ake yanzu, yawan kamfanonin kera kayayyaki masu hannun jari dake rukuni na A ko A-share a Turance, ya kai 2,121, wanda ya karu da kashi 69.7 bisa dari daga 1,250 a karshen shekarar 2017. Yayin da darajar manyan kamfanonin kera kayayyaki a kasuwa da aka zayyana, sun karu sosai daga shekarar 2017 zuwa ta 2021. Wadannan kamfanoni sun samu kudin shiga da yawansu ya kai yuan tiriliyan 11.79 kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 1.69, a cikin kudaden shiga na ayyukan da suka gudana a shekarar 2021, idan aka kwatanta da yuan tiriliyan 7.47 a shekarar 2017.

Wannan na kara nuna cewa, manufar kasar Sin ta bude kofa ga kasashen waje na kara amsa sunanta. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Tana Nacewa Ga Musanyar Bayanai Da Kasashen Ketare Ta Hanyar Da Ta Dace

Next Post

Kotu Ta Dakatar Da DSS Kan Cafke Shugaban Hukumar INEC

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

22 minutes ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

1 hour ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

2 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

4 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

5 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

6 hours ago
Next Post
Kotu Ta Dakatar Da DSS Kan Cafke Shugaban Hukumar INEC

Kotu Ta Dakatar Da DSS Kan Cafke Shugaban Hukumar INEC

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.