• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shari’ar ‘Yar Ganduje: Alkali Ya Umarci ‘Yan Jarida Su Fice Daga Cikin Kotu

by Abubakar Abba
3 years ago
in Labarai
0
Shari’ar ‘Yar Ganduje: Alkali Ya Umarci ‘Yan Jarida Su Fice Daga Cikin Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alkalin kotun shari’ar Musulunci da ke Jihar Kano, Abdullahi Halliru, ya umarci ‘yan jirida da su fice daga kotun domin Asiya-Balaraba Ganduje wato diya ga gwaman jihar, Ganduje, ta gabatar da takardar karar kashe aurenta da ta shafe shekara 16 da mijinta Inuwa Uba.

Ko da ya ke, alkalin ya ce, kowane mutum dai-dai ya ke da kowa a idon doka, inda ya kara da cewa, wannan karar ta musamman ce, wadda ba sai an wallafa ta ba, ganin irin mutanen da ke a cikin shari’ar.

  • Wasu Mutane Sun Kashe Wata Mata Sun Cefanar Da Sassan Jikinta A Jihar Ogun
  • 2023: ‘Yan Damfara Sun Bude Manhajar Intanet Don Daukar Ma’aikatan Zabe – INEC

Ya ce, zai yin wannan shari’ar ne a ofishinsa.

An ruwaito cewa, Balaraba ta bukaci kutun da ta raba aurenta bukatar bisa tsarin khul’i, kamar yadda shari’ar addinin musulunci ya tanada.

Mai sharia’a Khadi da ya yi dubi akan takadar karar, ya baiwa mijin wa’adin mako biyu da ya lalubo da hanyoyin da zai dai-dai da matarsa.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Khadin ya kuma kebe ranar 5 ga watan janairun 2023 domin ya yanke hukunci akan karar.

Sai dai, mijin Inuwa ya dage kai da fata cewa, har yanzu yana son matarsa tare da kuma bukatar kotun ta kara masa lokaci don ya samu ya shawo kan Balaraba.

An ruwaito cewa, a wasu shekarun baya, Balaraba ta samu sabani da mahaifanta saboda da koma wa bangaren mijinta wanda suka zarga da yin amfani da su don samun dukiyarsu.

Bugu da kari, an ruwaito wata majiya ta ce, bayan da Balaraba ta jure wa matsin da ta sha daga gun iyayenta ta kuma yi watsi da Inuwa, an tura jami’an tsaro zuwa gidan ma’auratan da ke a rukunin gidaje na Technical Staff, inda suka yi awon gaba da wasu takardun Ikadarorin Inuwa.

A cewar majiyar, kadarorin sun hada da na kan titin Kano zuwa Zaria da kuma takardun wasu gidajen sayar da man fetur da kuma wani gida da ke Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Diyar GandujeGandujekanoKotuRaba AureShari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

…Ko Goyon Bayan Da Peter Obi Ke Samu Zai Yi Tasiri?

Next Post

Qin Gang Ya Jaddada Muhimmancin Wanzar Da Daidaito A Dangantakar Sin Da Amurka

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

2 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

4 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

5 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

7 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

8 hours ago
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

9 hours ago
Next Post
Qin Gang Ya Jaddada Muhimmancin Wanzar Da Daidaito A Dangantakar Sin Da Amurka

Qin Gang Ya Jaddada Muhimmancin Wanzar Da Daidaito A Dangantakar Sin Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.