• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro Da Dama A Kaduna 

by Sadiq
3 years ago
Jami'an Tsaro

Wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Birnin Gwari a Jihar Kaduna, inda suka kashe jami’an tsaro da dama da suka hada da ‘yan sanda, sojoji da kuma ‘yan banga a wani shingen bincike a ranar Lahadi.

Wani mazaunin yankin, Abubakar Kakangi, ya shaida wa manema labarai a ranar Litinin cewa al’ummomin da abin ya shafa su ne kauyukan Kubau da Unguwan Zakara na karamar hukumar.

  • Tsohon Gwamnan Adamawa, Bindow Ya Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP
  • An Kubutar Da Mutum 6 Cikin Wadanda Aka Sace Yayin Harin Tashar Jirgin Kasa A Jihar Edo

A cewar Kakangi, ‘yan bindigar sun kulla yarjejeniya da manoman yankin a matsayin riga-kafi don bai wa mazauna yankin damar zuwa gonakinsu.

Sai dai ‘yan bindigar su kan bi ta kauyuka suna sayar da shanun da suka yi karo da su, lamarin da ya sanya jami’an tsaro tada girar sama.

A cewarsa, “Mako uku da suka gabata jami’an tsaro sun kashe wani yaro da ke kula da shanunsu (’yan bindiga), ba su ji dadin kashe yaron ba.

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

“Sai a jiya (Lahadi) ‘yan ta’addan sun kai hari a shingen bincike na Aka da ke kan titin Birnin-Gwari zuwa Kakangi zuwa Randagi a yammacin karamar hukumar Birnin-Gwari, inda suka farmaki duk wanda suka gani ciki har da jami’an tsaro.

“An kai harin ne da misalin karfe 2:00 na rana, ‘yan bindigar sun raba kawunansu gida biyu kuma sun kai harin a lokaci guda a kauyukan biyu, inda suka kashe jami’an tsaro da dama da suka hada da Civil Defence, ‘yansanda, ‘yan banga da sojoji.”

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga hukumar ‘yansanda ko wasu jami’an tsaro ko ma gwamnatin Jihar Kaduna kan lamarin.

A halin da ake ciki kuma, kiran da aka yi wa kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Muhammed Jalige, bai amsa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Next Post
NIS Ta Hukunta Jami’ai 36 Da Aka Kama Da Laifuka

NIS Ta Hukunta Jami'ai 36 Da Aka Kama Da Laifuka

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.