• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahaifina Ya Mika Kansa Ga ‘Yan Bindiga Suka Kashe Shi Don Ceton Rayuwarmu – Hajiya Asheku

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Hajiya Asheku, ‘yar marigayi Alhaji Zakari Umaru Kigbu, ta bayyana yadda ‘yan bindiga suka halaka mahaifinta, tsohon kwamishinan hukumar kidaya (NPC) a gidansa da ke garin Lafiya cikin Jihar Nasarawa.

Asheku ta ce misalin karfe 11 na dare ne maharan suka shigo gidansu, amma suka gagara balle kofan shiga dakin mahaifinta, don haka sai suka fara neman yara a gidan, ganin haka sai Alhaji Zajari Umaru Kigbu ya fito daga dakinsa ya fuskanci ‘yan bindigan a lokacin da ya lura sun gano yaransa a ban-daki kuma suka ta kokarin harbin su domin ya ki fitowa.

  • ‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

A ranar 28 ga watan Maris ne wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai hari gidan tsohon kwamishinan NPC, Zakari Umaru Kigbu, inda suka kashe shi, sannan suka sace dansa da kanwar matarsa. Kafin a kashe shi dai, Kigbu mai shekaru 60 da haihuwa kuma tsohon sojan saman mai ritaya yana koyarwa ne a kwalejin fasaha ta Isa Mustapha Agwai a Lafiya, (IMAP).

A yayin da ‘yan’uwa da abokan arziki ke ci gaba da jimamin rashin Alhaji Zakari Umar Kigbu, ‘yarsa mai shekara 29, Hajiya Asheku, cikin hawaye ta ba da labarin yadda makasan suka kashe mahaifinta ga ‘yan jarida.
Cikin kuka, Asheku ta ce, “Ni ce ta biyar cikin ‘ya’yan Zakari Umaru Kigbu kuma ‘yarsa mace tilo.
“A ranar da abin ya faru, ina zaune a falo a gidanmu da mahaifina da mahaifiyata da ‘yan’uwana muna kallon wani shiri a talabijin. Lokacin da muke kallon talabijin, mahaifina da mahaifiyata sun shiga dakinsu sun kwanta.
“Wasu cikin ‘yan’uwana suma sun ta fi sun kwanta, saboda abin ya faru ne misalin karfe 11 na dare.
“An bar ni a falo tare da dan’uwana wanda ke tura wasu abubuwa daga kwamfutarsa, kwatsam sai muka ji harbin bindiga. Daya cikin ‘yan’uwana ya yi maza ya rufe kofar kitchen da ta bulle tsakar gida.
“Wasu daga cikinmu mun ruga dakin mahaifinmu don mu boye, wasu kuma suka shiga dakin mahaifiyarmu.
“Yan bindigan, sun balle kofar gidanmu suka nufo dakin mahaifinmu. Da mahaifinmu ya lura dakinsa za su zo, sai ya umurci dukka mu mu fita mu ta fi store mu boye.
“Maharan sun yi kokarin balle kofar dakinsa, amma suka kasa saboda kofar na da karfi, sai suka fara neman mu.
“Da muka lura za su iya ganin mu cikin sauki a store, sai muka tafi ban-dakin mahaifyarmu muka boye, muna adduar Allah ya kawo mana dauki. Sun ta neman mu amma ba su gan mu ba.
“Suna cikin neman mu ne sai suka ji muna kus-kus a cikin ban-daki, nan take suka umurci mu fito ku su balle kofar su harbe mu dukkan mu. Saboda muna jin tsoro sai muka ki fitowa, sai suka umurci abokansu da ke waje su harbe mu ta tagar ban-daki. Sun fara harbe-harbe amma ba su same muba, domin duk mun kwanta.
“Ana hakan, mahaifinmu ya yi kokarin kiran ‘yan sanda da sojoji amma bai samu amsa mai gamsarwa ba. Don haka, ba shi da wata zabi sai ya fito daga dakinsa domin ya kare mu, a lokacin ne suka harbi mahaifina.
“Da muka ji karar harbin bindigan, dukkan mu mun fito waje muka gan shi kwance cikin jini.”
Asheku ta ce maharan su hudu ne kuma ba ta san ko harin na da alaka da siyasa ba.
Ta ce mahaifinta na harka da ‘yan siyasa, amma ba ta san dalilin da ya sa aka kawo masa harin ba
“Da suka zo, sun ce ba za su tafi ba sai sun kashe mahaifina a daren. Da suka harbe shi, dukkan mu mun fito mun gan shi cikin jinni, amma bai iya magana ba domin ya galabaita. Ya rasu bayan ‘yan mintuna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kun San Filin Kokowar Da Ke Kara Kyautata Zumuncin Sin Da Afirka?

Next Post

Daga Zuwa Neman Aure: “An Kashe Min Da, ‘Yansanda Sun Mayar Da Ni Saniyar Tatsa”

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

2 hours ago
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC
Manyan Labarai

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

2 hours ago
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
Labarai

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

4 hours ago
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
Manyan Labarai

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

8 hours ago
Kawayen amarya
Manyan Labarai

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

17 hours ago
Next Post
aure

Daga Zuwa Neman Aure: “An Kashe Min Da, ‘Yansanda Sun Mayar Da Ni Saniyar Tatsa”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

June 19, 2025
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

June 19, 2025
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

June 19, 2025
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.