ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahaifina Ya Mika Kansa Ga ‘Yan Bindiga Suka Kashe Shi Don Ceton Rayuwarmu – Hajiya Asheku

by Sulaiman
4 years ago
Bindiga

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Hajiya Asheku, ‘yar marigayi Alhaji Zakari Umaru Kigbu, ta bayyana yadda ‘yan bindiga suka halaka mahaifinta, tsohon kwamishinan hukumar kidaya (NPC) a gidansa da ke garin Lafiya cikin Jihar Nasarawa.

Asheku ta ce misalin karfe 11 na dare ne maharan suka shigo gidansu, amma suka gagara balle kofan shiga dakin mahaifinta, don haka sai suka fara neman yara a gidan, ganin haka sai Alhaji Zajari Umaru Kigbu ya fito daga dakinsa ya fuskanci ‘yan bindigan a lokacin da ya lura sun gano yaransa a ban-daki kuma suka ta kokarin harbin su domin ya ki fitowa.

  • ‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

A ranar 28 ga watan Maris ne wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai hari gidan tsohon kwamishinan NPC, Zakari Umaru Kigbu, inda suka kashe shi, sannan suka sace dansa da kanwar matarsa. Kafin a kashe shi dai, Kigbu mai shekaru 60 da haihuwa kuma tsohon sojan saman mai ritaya yana koyarwa ne a kwalejin fasaha ta Isa Mustapha Agwai a Lafiya, (IMAP).

ADVERTISEMENT

A yayin da ‘yan’uwa da abokan arziki ke ci gaba da jimamin rashin Alhaji Zakari Umar Kigbu, ‘yarsa mai shekara 29, Hajiya Asheku, cikin hawaye ta ba da labarin yadda makasan suka kashe mahaifinta ga ‘yan jarida.
Cikin kuka, Asheku ta ce, “Ni ce ta biyar cikin ‘ya’yan Zakari Umaru Kigbu kuma ‘yarsa mace tilo.
“A ranar da abin ya faru, ina zaune a falo a gidanmu da mahaifina da mahaifiyata da ‘yan’uwana muna kallon wani shiri a talabijin. Lokacin da muke kallon talabijin, mahaifina da mahaifiyata sun shiga dakinsu sun kwanta.
“Wasu cikin ‘yan’uwana suma sun ta fi sun kwanta, saboda abin ya faru ne misalin karfe 11 na dare.
“An bar ni a falo tare da dan’uwana wanda ke tura wasu abubuwa daga kwamfutarsa, kwatsam sai muka ji harbin bindiga. Daya cikin ‘yan’uwana ya yi maza ya rufe kofar kitchen da ta bulle tsakar gida.
“Wasu daga cikinmu mun ruga dakin mahaifinmu don mu boye, wasu kuma suka shiga dakin mahaifiyarmu.
“Yan bindigan, sun balle kofar gidanmu suka nufo dakin mahaifinmu. Da mahaifinmu ya lura dakinsa za su zo, sai ya umurci dukka mu mu fita mu ta fi store mu boye.
“Maharan sun yi kokarin balle kofar dakinsa, amma suka kasa saboda kofar na da karfi, sai suka fara neman mu.
“Da muka lura za su iya ganin mu cikin sauki a store, sai muka tafi ban-dakin mahaifyarmu muka boye, muna adduar Allah ya kawo mana dauki. Sun ta neman mu amma ba su gan mu ba.
“Suna cikin neman mu ne sai suka ji muna kus-kus a cikin ban-daki, nan take suka umurci mu fito ku su balle kofar su harbe mu dukkan mu. Saboda muna jin tsoro sai muka ki fitowa, sai suka umurci abokansu da ke waje su harbe mu ta tagar ban-daki. Sun fara harbe-harbe amma ba su same muba, domin duk mun kwanta.
“Ana hakan, mahaifinmu ya yi kokarin kiran ‘yan sanda da sojoji amma bai samu amsa mai gamsarwa ba. Don haka, ba shi da wata zabi sai ya fito daga dakinsa domin ya kare mu, a lokacin ne suka harbi mahaifina.
“Da muka ji karar harbin bindigan, dukkan mu mun fito waje muka gan shi kwance cikin jini.”
Asheku ta ce maharan su hudu ne kuma ba ta san ko harin na da alaka da siyasa ba.
Ta ce mahaifinta na harka da ‘yan siyasa, amma ba ta san dalilin da ya sa aka kawo masa harin ba
“Da suka zo, sun ce ba za su tafi ba sai sun kashe mahaifina a daren. Da suka harbe shi, dukkan mu mun fito mun gan shi cikin jinni, amma bai iya magana ba domin ya galabaita. Ya rasu bayan ‘yan mintuna.

Bindiga
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
aure

Daga Zuwa Neman Aure: “An Kashe Min Da, ‘Yansanda Sun Mayar Da Ni Saniyar Tatsa”

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.