ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahaifina Ya Mika Kansa Ga ‘Yan Bindiga Suka Kashe Shi Don Ceton Rayuwarmu – Hajiya Asheku

by Sulaiman
4 years ago
Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Hajiya Asheku, ‘yar marigayi Alhaji Zakari Umaru Kigbu, ta bayyana yadda ‘yan bindiga suka halaka mahaifinta, tsohon kwamishinan hukumar kidaya (NPC) a gidansa da ke garin Lafiya cikin Jihar Nasarawa.

Asheku ta ce misalin karfe 11 na dare ne maharan suka shigo gidansu, amma suka gagara balle kofan shiga dakin mahaifinta, don haka sai suka fara neman yara a gidan, ganin haka sai Alhaji Zajari Umaru Kigbu ya fito daga dakinsa ya fuskanci ‘yan bindigan a lokacin da ya lura sun gano yaransa a ban-daki kuma suka ta kokarin harbin su domin ya ki fitowa.

  • ‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

A ranar 28 ga watan Maris ne wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai hari gidan tsohon kwamishinan NPC, Zakari Umaru Kigbu, inda suka kashe shi, sannan suka sace dansa da kanwar matarsa. Kafin a kashe shi dai, Kigbu mai shekaru 60 da haihuwa kuma tsohon sojan saman mai ritaya yana koyarwa ne a kwalejin fasaha ta Isa Mustapha Agwai a Lafiya, (IMAP).

ADVERTISEMENT

A yayin da ‘yan’uwa da abokan arziki ke ci gaba da jimamin rashin Alhaji Zakari Umar Kigbu, ‘yarsa mai shekara 29, Hajiya Asheku, cikin hawaye ta ba da labarin yadda makasan suka kashe mahaifinta ga ‘yan jarida.
Cikin kuka, Asheku ta ce, “Ni ce ta biyar cikin ‘ya’yan Zakari Umaru Kigbu kuma ‘yarsa mace tilo.
“A ranar da abin ya faru, ina zaune a falo a gidanmu da mahaifina da mahaifiyata da ‘yan’uwana muna kallon wani shiri a talabijin. Lokacin da muke kallon talabijin, mahaifina da mahaifiyata sun shiga dakinsu sun kwanta.
“Wasu cikin ‘yan’uwana suma sun ta fi sun kwanta, saboda abin ya faru ne misalin karfe 11 na dare.
“An bar ni a falo tare da dan’uwana wanda ke tura wasu abubuwa daga kwamfutarsa, kwatsam sai muka ji harbin bindiga. Daya cikin ‘yan’uwana ya yi maza ya rufe kofar kitchen da ta bulle tsakar gida.
“Wasu daga cikinmu mun ruga dakin mahaifinmu don mu boye, wasu kuma suka shiga dakin mahaifiyarmu.
“Yan bindigan, sun balle kofar gidanmu suka nufo dakin mahaifinmu. Da mahaifinmu ya lura dakinsa za su zo, sai ya umurci dukka mu mu fita mu ta fi store mu boye.
“Maharan sun yi kokarin balle kofar dakinsa, amma suka kasa saboda kofar na da karfi, sai suka fara neman mu.
“Da muka lura za su iya ganin mu cikin sauki a store, sai muka tafi ban-dakin mahaifyarmu muka boye, muna adduar Allah ya kawo mana dauki. Sun ta neman mu amma ba su gan mu ba.
“Suna cikin neman mu ne sai suka ji muna kus-kus a cikin ban-daki, nan take suka umurci mu fito ku su balle kofar su harbe mu dukkan mu. Saboda muna jin tsoro sai muka ki fitowa, sai suka umurci abokansu da ke waje su harbe mu ta tagar ban-daki. Sun fara harbe-harbe amma ba su same muba, domin duk mun kwanta.
“Ana hakan, mahaifinmu ya yi kokarin kiran ‘yan sanda da sojoji amma bai samu amsa mai gamsarwa ba. Don haka, ba shi da wata zabi sai ya fito daga dakinsa domin ya kare mu, a lokacin ne suka harbi mahaifina.
“Da muka ji karar harbin bindigan, dukkan mu mun fito waje muka gan shi kwance cikin jini.”
Asheku ta ce maharan su hudu ne kuma ba ta san ko harin na da alaka da siyasa ba.
Ta ce mahaifinta na harka da ‘yan siyasa, amma ba ta san dalilin da ya sa aka kawo masa harin ba
“Da suka zo, sun ce ba za su tafi ba sai sun kashe mahaifina a daren. Da suka harbe shi, dukkan mu mun fito mun gan shi cikin jinni, amma bai iya magana ba domin ya galabaita. Ya rasu bayan ‘yan mintuna.

Bindiga
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
aure

Daga Zuwa Neman Aure: “An Kashe Min Da, ‘Yansanda Sun Mayar Da Ni Saniyar Tatsa”

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.