• Leadership Hausa
Thursday, August 18, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Mahaifina Ya Mika Kansa Ga ‘Yan Bindiga Suka Kashe Shi Don Ceton Rayuwarmu – Hajiya Asheku

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Shingen Bincike Na ‘Yan Sanda Sun Harbe Mutum 2 A Ebonyi

Ku Yi Watsi Da Masu Wa’azin Son Wargaza Hadin Kan Nijeriya —IBB

Hajiya Asheku, ‘yar marigayi Alhaji Zakari Umaru Kigbu, ta bayyana yadda ‘yan bindiga suka halaka mahaifinta, tsohon kwamishinan hukumar kidaya (NPC) a gidansa da ke garin Lafiya cikin Jihar Nasarawa.

Asheku ta ce misalin karfe 11 na dare ne maharan suka shigo gidansu, amma suka gagara balle kofan shiga dakin mahaifinta, don haka sai suka fara neman yara a gidan, ganin haka sai Alhaji Zajari Umaru Kigbu ya fito daga dakinsa ya fuskanci ‘yan bindigan a lokacin da ya lura sun gano yaransa a ban-daki kuma suka ta kokarin harbin su domin ya ki fitowa.

  • ‘Yan bindiga Sun Kai Hari Kauyuka 8 Da Kashe 33 Da Sace Mutum 30 Da Shanu 2,000 A Kebbi Da Neja,

A ranar 28 ga watan Maris ne wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai hari gidan tsohon kwamishinan NPC, Zakari Umaru Kigbu, inda suka kashe shi, sannan suka sace dansa da kanwar matarsa. Kafin a kashe shi dai, Kigbu mai shekaru 60 da haihuwa kuma tsohon sojan saman mai ritaya yana koyarwa ne a kwalejin fasaha ta Isa Mustapha Agwai a Lafiya, (IMAP).

A yayin da ‘yan’uwa da abokan arziki ke ci gaba da jimamin rashin Alhaji Zakari Umar Kigbu, ‘yarsa mai shekara 29, Hajiya Asheku, cikin hawaye ta ba da labarin yadda makasan suka kashe mahaifinta ga ‘yan jarida.
Cikin kuka, Asheku ta ce, “Ni ce ta biyar cikin ‘ya’yan Zakari Umaru Kigbu kuma ‘yarsa mace tilo.
“A ranar da abin ya faru, ina zaune a falo a gidanmu da mahaifina da mahaifiyata da ‘yan’uwana muna kallon wani shiri a talabijin. Lokacin da muke kallon talabijin, mahaifina da mahaifiyata sun shiga dakinsu sun kwanta.
“Wasu cikin ‘yan’uwana suma sun ta fi sun kwanta, saboda abin ya faru ne misalin karfe 11 na dare.
“An bar ni a falo tare da dan’uwana wanda ke tura wasu abubuwa daga kwamfutarsa, kwatsam sai muka ji harbin bindiga. Daya cikin ‘yan’uwana ya yi maza ya rufe kofar kitchen da ta bulle tsakar gida.
“Wasu daga cikinmu mun ruga dakin mahaifinmu don mu boye, wasu kuma suka shiga dakin mahaifiyarmu.
“Yan bindigan, sun balle kofar gidanmu suka nufo dakin mahaifinmu. Da mahaifinmu ya lura dakinsa za su zo, sai ya umurci dukka mu mu fita mu ta fi store mu boye.
“Maharan sun yi kokarin balle kofar dakinsa, amma suka kasa saboda kofar na da karfi, sai suka fara neman mu.
“Da muka lura za su iya ganin mu cikin sauki a store, sai muka tafi ban-dakin mahaifyarmu muka boye, muna adduar Allah ya kawo mana dauki. Sun ta neman mu amma ba su gan mu ba.
“Suna cikin neman mu ne sai suka ji muna kus-kus a cikin ban-daki, nan take suka umurci mu fito ku su balle kofar su harbe mu dukkan mu. Saboda muna jin tsoro sai muka ki fitowa, sai suka umurci abokansu da ke waje su harbe mu ta tagar ban-daki. Sun fara harbe-harbe amma ba su same muba, domin duk mun kwanta.
“Ana hakan, mahaifinmu ya yi kokarin kiran ‘yan sanda da sojoji amma bai samu amsa mai gamsarwa ba. Don haka, ba shi da wata zabi sai ya fito daga dakinsa domin ya kare mu, a lokacin ne suka harbi mahaifina.
“Da muka ji karar harbin bindigan, dukkan mu mun fito waje muka gan shi kwance cikin jini.”
Asheku ta ce maharan su hudu ne kuma ba ta san ko harin na da alaka da siyasa ba.
Ta ce mahaifinta na harka da ‘yan siyasa, amma ba ta san dalilin da ya sa aka kawo masa harin ba
“Da suka zo, sun ce ba za su tafi ba sai sun kashe mahaifina a daren. Da suka harbe shi, dukkan mu mun fito mun gan shi cikin jinni, amma bai iya magana ba domin ya galabaita. Ya rasu bayan ‘yan mintuna.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kun San Filin Kokowar Da Ke Kara Kyautata Zumuncin Sin Da Afirka?

Next Post

Daga Zuwa Neman Aure: “An Kashe Min Da, ‘Yansanda Sun Mayar Da Ni Saniyar Tatsa”

Related

Fada Ya Barke Tsakanin Shugabannin ’Yan Bindiga, 2 Sun Mutu Yayin Rikicin A Zamfara
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Shingen Bincike Na ‘Yan Sanda Sun Harbe Mutum 2 A Ebonyi

3 hours ago
Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.
Labarai

Ku Yi Watsi Da Masu Wa’azin Son Wargaza Hadin Kan Nijeriya —IBB

4 hours ago
Kungiyar Haɗin Kan Musulunci ta Duniya Ta Ziyarci Medina Baye Niass
Labarai

Kungiyar Haɗin Kan Musulunci ta Duniya Ta Ziyarci Medina Baye Niass

5 hours ago
Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.
Rahotonni

Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.

5 hours ago
Majalisar Jihar Zamfara Ta Zartar Da Dokar Kariya Ga Masu Bukata Ta Musanman
Manyan Labarai

Matawalle Ya Amince Da Hukuncin Kisa Kan Masu Garkuwa Da Masu Ba ‘Yan Bindiga Bayanan Sirri

17 hours ago
Labarai

Ma’aikatan Wutar Lantarki Sun Janye Yajin Aikin Da Suka Fara Na Mako 2

17 hours ago
Next Post
aure

Daga Zuwa Neman Aure: “An Kashe Min Da, ‘Yansanda Sun Mayar Da Ni Saniyar Tatsa”

LABARAI MASU NASABA

Fada Ya Barke Tsakanin Shugabannin ’Yan Bindiga, 2 Sun Mutu Yayin Rikicin A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Shingen Bincike Na ‘Yan Sanda Sun Harbe Mutum 2 A Ebonyi

August 18, 2022
An Cafke Mutumin Da Zai Aike Da Bindigu Kano Daga Abuja Ta Tashar Mota

An Cafke Mutumin Da Zai Aike Da Bindigu Kano Daga Abuja Ta Tashar Mota

August 18, 2022
Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.

Ku Yi Watsi Da Masu Wa’azin Son Wargaza Hadin Kan Nijeriya —IBB

August 18, 2022
Kungiyar Haɗin Kan Musulunci ta Duniya Ta Ziyarci Medina Baye Niass

Kungiyar Haɗin Kan Musulunci ta Duniya Ta Ziyarci Medina Baye Niass

August 18, 2022
Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.

Neman ‘Yancin Nijeriya: Dr Nnamdi Azikiwe da Ahmed Mahmud Saad Zungur A Landan.

August 18, 2022
Majalisar Jihar Zamfara Ta Zartar Da Dokar Kariya Ga Masu Bukata Ta Musanman

Matawalle Ya Amince Da Hukuncin Kisa Kan Masu Garkuwa Da Masu Ba ‘Yan Bindiga Bayanan Sirri

August 17, 2022

Ma’aikatan Wutar Lantarki Sun Janye Yajin Aikin Da Suka Fara Na Mako 2

August 17, 2022
Kudin Shigar Manyan Kamfanonin Kera Na’urorin Sadarwa Na Sin Ya Kai Yuan Triliyan 14 A 2021

Kudin Shigar Manyan Kamfanonin Kera Na’urorin Sadarwa Na Sin Ya Kai Yuan Triliyan 14 A 2021

August 17, 2022
Yanayin Kare Hakkin Dan Adam Na ‘Yan Kananan Kabilun Sin Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

Yanayin Kare Hakkin Dan Adam Na ‘Yan Kananan Kabilun Sin Ya Kai Matsayin Koli A Tarihi

August 17, 2022
Gaskiya Ba Ta Buya…

Gaskiya Ba Ta Buya…

August 17, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.