• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Gwangwaje Kananan Ma’aikatan Jihar Da Sabbin Gidaje 460

by Hussein Yero
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Gwangwaje Kananan Ma’aikatan Jihar Da Sabbin Gidaje 460
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya mika gidaje dari hudu da sittin (460) ga kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) reshen jihar Zamfara, domin rabawa kananan ma’aikata a jihar.

Gwamna Matawalle ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a wajen bikin na mika rukunin gidajen da ke kan titin Gidan Dawa Daza a Gusau, babban birnin jihar.

  • 2023: Zan Dora Daga Inda Na Tsaya Idan Na Zarce – Matawalle
  • Gwamnatin Zamfara Ta Gano Likitocin Bogi 199 A Jihar

Gwamnan ya bayyana cewa samar da gidajen na daya daga cikin kokarin gwamnatinsa na samar da wurin kwana na dindindin ga ma’aikatan gwamnati a jihar manyan da kananansu”.

“Ya kara da cewa, baya ga samar da gidaje dari hudu da sittin da aka kammala na kananan ma’aikata, za a sake gina wasu gidaje 1000 ga manyan ma’aikatan gwamnati a fadin jihar, inda ya yi nuni da cewa a cikin makon nan ne zai yi bikin kaddamar da harsashin ginin ma’aikatan.

Matwalle ya ce za a gina gidaje dubu daya a Gusau, da nufin magance kalubalen wurin kwana na manyan da kananan ma’aikata a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

“Matawalen ya bayyana matukar damuwarsa kan yadda ma’aikatan gwamnati ke yin ritaya bayan shekaru talatin da biyar suna aiki ba tare da sun mallaki gida ba, wannan ya ce gwamnatinsa za ta magance hakan ta hanyar gina musu gidajan.

A cewar Gwamnan, rukunin farko da na biyu na gidajen da suka kai dari hudu da sittin za a raba su ne ga ma’aikata tare da rage kashi arba’in cikin dari na jimillar kudaden da za a biya cikin shekaru goma.

Gwamna Bello Matawalle ya yi kira ga shugabannin kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) da su hada kai da ofishin shugaban ma’aikata na jiha da kuma hukumar kula da harkokin kwadago domin tabbatar da adalci wajen rabon gidajen domin amfanar ma’aikatan gwamnati.

Shugaban Kungiyar Kwadago ta Nijeriya, Kwamared Sani Halliru Magajin Rafin Kurya, ya bayyana jin dadinsa ga Gwamnan bisa shirinsa na samar da gidajen kwana ga ma’aikatan da ke aiki.

Kwamared Sani Halliru, a madadin daukacin ma’aikatan jihar ya godewa gwamnan kan yadda ya ceto dubban ma’aikata da iyalansu daga matsalar rashin matsuguni musamman bayan ritayar da suka yi tare da tabbatar wa Gwamna Matawalle goyon bayan ma’aikata da hadin kai domin gwamnatinsa ta samu nasara ga kowa da kowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Jajanta Wa Rundunar ‘Yansandan Kano Kan Gobarar Da Ta Tashi A Ofishinta

Next Post

‘Yan Ta’addar Da Suka Yi Garkuwa Da DPO A Jihar Filato Sun Sake Shi

Related

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”
Manyan Labarai

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

41 minutes ago
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

2 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

6 hours ago
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu
Manyan Labarai

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

8 hours ago
Next Post
Mutum 25 Ne Suka Bace Cikin Wata 6 A Jihar Abia — ‘Yan Sanda

'Yan Ta'addar Da Suka Yi Garkuwa Da DPO A Jihar Filato Sun Sake Shi

LABARAI MASU NASABA

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.