ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Gwangwaje Kananan Ma’aikatan Jihar Da Sabbin Gidaje 460

by Hussein Yero
4 years ago
Gwamnatin

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya mika gidaje dari hudu da sittin (460) ga kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) reshen jihar Zamfara, domin rabawa kananan ma’aikata a jihar.

Gwamna Matawalle ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a wajen bikin na mika rukunin gidajen da ke kan titin Gidan Dawa Daza a Gusau, babban birnin jihar.

  • 2023: Zan Dora Daga Inda Na Tsaya Idan Na Zarce – Matawalle
  • Gwamnatin Zamfara Ta Gano Likitocin Bogi 199 A Jihar

Gwamnan ya bayyana cewa samar da gidajen na daya daga cikin kokarin gwamnatinsa na samar da wurin kwana na dindindin ga ma’aikatan gwamnati a jihar manyan da kananansu”.

ADVERTISEMENT

“Ya kara da cewa, baya ga samar da gidaje dari hudu da sittin da aka kammala na kananan ma’aikata, za a sake gina wasu gidaje 1000 ga manyan ma’aikatan gwamnati a fadin jihar, inda ya yi nuni da cewa a cikin makon nan ne zai yi bikin kaddamar da harsashin ginin ma’aikatan.

Matwalle ya ce za a gina gidaje dubu daya a Gusau, da nufin magance kalubalen wurin kwana na manyan da kananan ma’aikata a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

“Matawalen ya bayyana matukar damuwarsa kan yadda ma’aikatan gwamnati ke yin ritaya bayan shekaru talatin da biyar suna aiki ba tare da sun mallaki gida ba, wannan ya ce gwamnatinsa za ta magance hakan ta hanyar gina musu gidajan.

A cewar Gwamnan, rukunin farko da na biyu na gidajen da suka kai dari hudu da sittin za a raba su ne ga ma’aikata tare da rage kashi arba’in cikin dari na jimillar kudaden da za a biya cikin shekaru goma.

Gwamna Bello Matawalle ya yi kira ga shugabannin kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) da su hada kai da ofishin shugaban ma’aikata na jiha da kuma hukumar kula da harkokin kwadago domin tabbatar da adalci wajen rabon gidajen domin amfanar ma’aikatan gwamnati.

Shugaban Kungiyar Kwadago ta Nijeriya, Kwamared Sani Halliru Magajin Rafin Kurya, ya bayyana jin dadinsa ga Gwamnan bisa shirinsa na samar da gidajen kwana ga ma’aikatan da ke aiki.

Kwamared Sani Halliru, a madadin daukacin ma’aikatan jihar ya godewa gwamnan kan yadda ya ceto dubban ma’aikata da iyalansu daga matsalar rashin matsuguni musamman bayan ritayar da suka yi tare da tabbatar wa Gwamna Matawalle goyon bayan ma’aikata da hadin kai domin gwamnatinsa ta samu nasara ga kowa da kowa.

Gwamnatin
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara

MASU ALAKA

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta
Labarai

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Next Post
Mutum 25 Ne Suka Bace Cikin Wata 6 A Jihar Abia — ‘Yan Sanda

'Yan Ta'addar Da Suka Yi Garkuwa Da DPO A Jihar Filato Sun Sake Shi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

An Rufe Babban Taron AI Na Duniya Na 2026

July 21, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Zargin Satar Shanu A Bauchi, Sun Ƙwato Bijimi 3

July 21, 2026
Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida

July 21, 2026
Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

Nasarawa Na Sa Ran Samun Dala Miliyan 10 Daga Lithium Kafin Karshen Shekara – Gwamna Sule

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.