• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Kama Emefiele Ba – DSS

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Ba Mu Kama Emefiele Ba – DSS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), ta ce ba ta kai mamaya ofishin Babban Bankin Nijeriya ba kamar yadda wasu rahotanni suka nuna.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar DSS, Peter Afunanya ya fitar, ya kuma ce rundunar ‘yan sandan sirrin ba ta kama gwamnan CBN, Godwin Emefiele ba.

  • Musulman Sun Fusata Da Matakin Gwamnatin Bauchi Kan Makabarta
  • DSS Ta Karyata Yin Kawanya A Shalkwar CBN, Bayan Emefiele Ya Dawo Kan Aiki

Da yake karyata rahotannin da kafafen yada labarai suka yada na kama shi, kakakin DSS, ya bayyana hakan a matsayin labaran bogi.

“An jawo hankalin Hukumar Tsaro Farin Kaya (DSS) kan labarin karya da ake yadawa cewa jami’anta sun mamaye Babban Bankin Nijeriya tare da kama gwamnansa, a yau 16/1/23. Wannan labari ne na karya kuma yaudara ce,” in ji sanarwar.

A halin yanzu dai Emefiele ya koma bakin aikinsa bayan hutun da ya yi a kasar waje.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

Daraktan Sadarwa na CBN, Osita Nwanisobi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Litinin.

Sanarwar ta kara da cewa, “Gwamnan babban bankin ya koma aiki tare da sabunta kwarin guiwa don gudanar da aikinsa gabanin taron kwamitin kula da harkokin kudi na farko (MPC) na shekarar nan a ranar 23 zuwa 24 ga watan Janairu, 2023,” in ji sanarwar.

“Emefiele ya ci gaba da jajircewa wajen gudanar da aikin da ke gabansa daidai don tsarin manufofin shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

A kwanakin baya ne dai DSS ta sanya wa Emefiele kahon zuka wanda suka kai kara kotu bisa zarginsa sa daukar nauyin ta’addanci.

DSS ta garzaya wata kotun Abuja domin samun sahalewa don ta kamo gwamnan babban bankin bisa zargin daukar nauyin ta’addanci da kuma laifukan da suka shafi tattalin arzikin kasa, amma mai shari’a Maryam Hassan ta babbar kotun, ta yi watsi da bukatar ta DSS.

Bayan haka, alkalin ta DSS kama, gayyata, ko tsare Emefiele, inda ta bayyana zargin ta’addancin da DSS ke yiwa gwamnan CBN a matsayin daukar zargi mara tushe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNDaukar NauyiDSSGodwin EmefieleMamayaTa'addanciZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Musulmai Sun Fusata Da Matakin Gwamnatin Bauchi Kan Makabarta

Next Post

Akwai Hatsarin Gaske Mika Mulkin Nijeriya A Hannun Tinubu ko Obi – Atiku 

Related

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

20 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

1 day ago
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Manyan Labarai

Ina Aka Kwana Batun Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Dazukan Jihar Katsina?

1 day ago
Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori
Manyan Labarai

Dubban Matasan Kano Sun Yi Zanga-zangar Lumana Domin Goyon Bayan CP AI Bakori

2 days ago
Next Post
Ya Kamata CBN Ya Sanya Hoton Obasanjo A Jikin Sabbin Kudin Da Za A Sauya Wa Fasali

Akwai Hatsarin Gaske Mika Mulkin Nijeriya A Hannun Tinubu ko Obi - Atiku 

LABARAI MASU NASABA

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

Illolin Da Ke Tattare Da Mallaka Wa Kananan Yara Wayar Hannu

October 4, 2025
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

October 4, 2025
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.