• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Nijeriya

Shugaban rundunar tsaro ta kasa, Janaral Lucky Irabor ya bayyana cewa dimokuradiyya ta zauna daram da kafarta a Nijeriya babau batun juyin mulki.

Ya ce rundunar sojojin Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro na kasa wajen tabbatar da an gudanar da zaben 2023 a cikin kwanciyar hankali da lumana.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • Kuskuren Shugabannin Baya Ne Ya Jefa Nijeriya Cikin Tsaka Mai Wuya – Kwankwaso

Shugaban rundunar tsaron ya bayyana hakan ne a wurin tunawa da jaruman sojojin da suka mutu a lokacin yaki na 2023, wanda ya gudana a Abuja.

Irabor ya ce, “Za mu tabbatar da cewa rundunar sojojin Nijeriya ta hada kai da ‘yansanda domin bayar da cikakken goyon baya wajen gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da lumana.”

Da yake amsa tambayoyin manema labarai dangane da shirye-shiryen sojoji kan zaben 2023, ya ce duk da jami’an ‘yansanda ne sahun gaba a lokacin zabe, sojoji za su mara musu baya domin ganin an gudanar da zabe lami lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

“Na tabbar da cewa kun san ‘yansanda ne suke kan gaba wurin bayar da tsaro lokacin zabe. Na tattauna da babban sufetan ‘yansanda kan irin gudummuwar da za mu iya bayarwa wajen tallafa wa ‘yansanda lokacin zabe.

“Ina mai tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa rundunar sojojin Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yansanda domin bayar da duk wata gudummuwa da ‘yansanda ke bukata.”

Ya kuma tabbata wa ‘yan Nijeriya cewa dimokuradiyya a kasar nan ba ta wata samun barazana daga juyin mulkin sojoji kamar yadda aka samu a wasu kasashen Afirka.

“Dimokuradiyya ta zauna daram da kafarta. Ta kasance gwamnati ta mutane, kuma ta jama’ar Nijeriya wacce ta zauna daram da kafafunta,” in ji shi.

Har ila yau, Irabor ya siffanta wannan bikin tunawa da gwarazan sojoji a matsayin sadaukarwa ga wadanda suke ganin su mutu domin kasarsu.

Ya ce “Bikin ba ranar tunawa da mamatan ba ne, ya kasance ranar da za mu nuna godiyarmu ga Allah mazanmu da matanmu wajen yin hidima ga kasarmu, kuma za mu ci gaba da hidinta wa kasar nan.

“Muna daukar irin wannan mataki wajen nuna soyayya ga kasarmu mazanmu da matanmu, wanda hakan ne ma ya sa akwai bukatar sadaukar da kai domin sauran mu su rayu. Ina ganin wannan shi ne ya fi cancanta.”

Tun da farko, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi nazari kan bikin na karshe a matsayinsa na shugaban askarawan Nijeriya, a daidai lokacin da zai cika shekara takwas a kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya jagoranci manyan jami’an gwamnati a wajen kaddamar da bikin karshe na tunawa da gwarazon sojoji na wannan shekara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nijeriya
Manyan Labarai

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Next Post
Za A Fara Kidayar ‘Yan Nijeriya A Watan Maris – NPC

Za A Fara Kidayar 'Yan Nijeriya A Watan Maris - NPC

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.