ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Nijeriya

Shugaban rundunar tsaro ta kasa, Janaral Lucky Irabor ya bayyana cewa dimokuradiyya ta zauna daram da kafarta a Nijeriya babau batun juyin mulki.

Ya ce rundunar sojojin Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro na kasa wajen tabbatar da an gudanar da zaben 2023 a cikin kwanciyar hankali da lumana.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • Kuskuren Shugabannin Baya Ne Ya Jefa Nijeriya Cikin Tsaka Mai Wuya – Kwankwaso

Shugaban rundunar tsaron ya bayyana hakan ne a wurin tunawa da jaruman sojojin da suka mutu a lokacin yaki na 2023, wanda ya gudana a Abuja.

ADVERTISEMENT

Irabor ya ce, “Za mu tabbatar da cewa rundunar sojojin Nijeriya ta hada kai da ‘yansanda domin bayar da cikakken goyon baya wajen gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da lumana.”

Da yake amsa tambayoyin manema labarai dangane da shirye-shiryen sojoji kan zaben 2023, ya ce duk da jami’an ‘yansanda ne sahun gaba a lokacin zabe, sojoji za su mara musu baya domin ganin an gudanar da zabe lami lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

“Na tabbar da cewa kun san ‘yansanda ne suke kan gaba wurin bayar da tsaro lokacin zabe. Na tattauna da babban sufetan ‘yansanda kan irin gudummuwar da za mu iya bayarwa wajen tallafa wa ‘yansanda lokacin zabe.

“Ina mai tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa rundunar sojojin Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yansanda domin bayar da duk wata gudummuwa da ‘yansanda ke bukata.”

Ya kuma tabbata wa ‘yan Nijeriya cewa dimokuradiyya a kasar nan ba ta wata samun barazana daga juyin mulkin sojoji kamar yadda aka samu a wasu kasashen Afirka.

“Dimokuradiyya ta zauna daram da kafarta. Ta kasance gwamnati ta mutane, kuma ta jama’ar Nijeriya wacce ta zauna daram da kafafunta,” in ji shi.

Har ila yau, Irabor ya siffanta wannan bikin tunawa da gwarazan sojoji a matsayin sadaukarwa ga wadanda suke ganin su mutu domin kasarsu.

Ya ce “Bikin ba ranar tunawa da mamatan ba ne, ya kasance ranar da za mu nuna godiyarmu ga Allah mazanmu da matanmu wajen yin hidima ga kasarmu, kuma za mu ci gaba da hidinta wa kasar nan.

“Muna daukar irin wannan mataki wajen nuna soyayya ga kasarmu mazanmu da matanmu, wanda hakan ne ma ya sa akwai bukatar sadaukar da kai domin sauran mu su rayu. Ina ganin wannan shi ne ya fi cancanta.”

Tun da farko, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi nazari kan bikin na karshe a matsayinsa na shugaban askarawan Nijeriya, a daidai lokacin da zai cika shekara takwas a kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya jagoranci manyan jami’an gwamnati a wajen kaddamar da bikin karshe na tunawa da gwarazon sojoji na wannan shekara.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Next Post
Za A Fara Kidayar ‘Yan Nijeriya A Watan Maris – NPC

Za A Fara Kidayar 'Yan Nijeriya A Watan Maris - NPC

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.