ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Nijeriya

Shugaban rundunar tsaro ta kasa, Janaral Lucky Irabor ya bayyana cewa dimokuradiyya ta zauna daram da kafarta a Nijeriya babau batun juyin mulki.

Ya ce rundunar sojojin Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro na kasa wajen tabbatar da an gudanar da zaben 2023 a cikin kwanciyar hankali da lumana.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • Kuskuren Shugabannin Baya Ne Ya Jefa Nijeriya Cikin Tsaka Mai Wuya – Kwankwaso

Shugaban rundunar tsaron ya bayyana hakan ne a wurin tunawa da jaruman sojojin da suka mutu a lokacin yaki na 2023, wanda ya gudana a Abuja.

ADVERTISEMENT

Irabor ya ce, “Za mu tabbatar da cewa rundunar sojojin Nijeriya ta hada kai da ‘yansanda domin bayar da cikakken goyon baya wajen gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da lumana.”

Da yake amsa tambayoyin manema labarai dangane da shirye-shiryen sojoji kan zaben 2023, ya ce duk da jami’an ‘yansanda ne sahun gaba a lokacin zabe, sojoji za su mara musu baya domin ganin an gudanar da zabe lami lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Na tabbar da cewa kun san ‘yansanda ne suke kan gaba wurin bayar da tsaro lokacin zabe. Na tattauna da babban sufetan ‘yansanda kan irin gudummuwar da za mu iya bayarwa wajen tallafa wa ‘yansanda lokacin zabe.

“Ina mai tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa rundunar sojojin Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yansanda domin bayar da duk wata gudummuwa da ‘yansanda ke bukata.”

Ya kuma tabbata wa ‘yan Nijeriya cewa dimokuradiyya a kasar nan ba ta wata samun barazana daga juyin mulkin sojoji kamar yadda aka samu a wasu kasashen Afirka.

“Dimokuradiyya ta zauna daram da kafarta. Ta kasance gwamnati ta mutane, kuma ta jama’ar Nijeriya wacce ta zauna daram da kafafunta,” in ji shi.

Har ila yau, Irabor ya siffanta wannan bikin tunawa da gwarazan sojoji a matsayin sadaukarwa ga wadanda suke ganin su mutu domin kasarsu.

Ya ce “Bikin ba ranar tunawa da mamatan ba ne, ya kasance ranar da za mu nuna godiyarmu ga Allah mazanmu da matanmu wajen yin hidima ga kasarmu, kuma za mu ci gaba da hidinta wa kasar nan.

“Muna daukar irin wannan mataki wajen nuna soyayya ga kasarmu mazanmu da matanmu, wanda hakan ne ma ya sa akwai bukatar sadaukar da kai domin sauran mu su rayu. Ina ganin wannan shi ne ya fi cancanta.”

Tun da farko, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi nazari kan bikin na karshe a matsayinsa na shugaban askarawan Nijeriya, a daidai lokacin da zai cika shekara takwas a kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya jagoranci manyan jami’an gwamnati a wajen kaddamar da bikin karshe na tunawa da gwarazon sojoji na wannan shekara.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Za A Fara Kidayar ‘Yan Nijeriya A Watan Maris – NPC

Za A Fara Kidayar 'Yan Nijeriya A Watan Maris - NPC

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.