ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Nijeriya

Shugaban rundunar tsaro ta kasa, Janaral Lucky Irabor ya bayyana cewa dimokuradiyya ta zauna daram da kafarta a Nijeriya babau batun juyin mulki.

Ya ce rundunar sojojin Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro na kasa wajen tabbatar da an gudanar da zaben 2023 a cikin kwanciyar hankali da lumana.

  • Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 
  • Kuskuren Shugabannin Baya Ne Ya Jefa Nijeriya Cikin Tsaka Mai Wuya – Kwankwaso

Shugaban rundunar tsaron ya bayyana hakan ne a wurin tunawa da jaruman sojojin da suka mutu a lokacin yaki na 2023, wanda ya gudana a Abuja.

ADVERTISEMENT

Irabor ya ce, “Za mu tabbatar da cewa rundunar sojojin Nijeriya ta hada kai da ‘yansanda domin bayar da cikakken goyon baya wajen gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da lumana.”

Da yake amsa tambayoyin manema labarai dangane da shirye-shiryen sojoji kan zaben 2023, ya ce duk da jami’an ‘yansanda ne sahun gaba a lokacin zabe, sojoji za su mara musu baya domin ganin an gudanar da zabe lami lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Na tabbar da cewa kun san ‘yansanda ne suke kan gaba wurin bayar da tsaro lokacin zabe. Na tattauna da babban sufetan ‘yansanda kan irin gudummuwar da za mu iya bayarwa wajen tallafa wa ‘yansanda lokacin zabe.

“Ina mai tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa rundunar sojojin Nijeriya za ta yi aiki kafada da kafada da ‘yansanda domin bayar da duk wata gudummuwa da ‘yansanda ke bukata.”

Ya kuma tabbata wa ‘yan Nijeriya cewa dimokuradiyya a kasar nan ba ta wata samun barazana daga juyin mulkin sojoji kamar yadda aka samu a wasu kasashen Afirka.

“Dimokuradiyya ta zauna daram da kafarta. Ta kasance gwamnati ta mutane, kuma ta jama’ar Nijeriya wacce ta zauna daram da kafafunta,” in ji shi.

Har ila yau, Irabor ya siffanta wannan bikin tunawa da gwarazan sojoji a matsayin sadaukarwa ga wadanda suke ganin su mutu domin kasarsu.

Ya ce “Bikin ba ranar tunawa da mamatan ba ne, ya kasance ranar da za mu nuna godiyarmu ga Allah mazanmu da matanmu wajen yin hidima ga kasarmu, kuma za mu ci gaba da hidinta wa kasar nan.

“Muna daukar irin wannan mataki wajen nuna soyayya ga kasarmu mazanmu da matanmu, wanda hakan ne ma ya sa akwai bukatar sadaukar da kai domin sauran mu su rayu. Ina ganin wannan shi ne ya fi cancanta.”

Tun da farko, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi nazari kan bikin na karshe a matsayinsa na shugaban askarawan Nijeriya, a daidai lokacin da zai cika shekara takwas a kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ya jagoranci manyan jami’an gwamnati a wajen kaddamar da bikin karshe na tunawa da gwarazon sojoji na wannan shekara.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Za A Fara Kidayar ‘Yan Nijeriya A Watan Maris – NPC

Za A Fara Kidayar 'Yan Nijeriya A Watan Maris - NPC

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.