ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 

by CMG Hausa
3 years ago
Sin da Afirka

A bayan garin birnin Addis Ababa na kasar Habasha, akwai jerin wasu gine-gine masu salo na musamman, wadanda suke matukar jan hankalin al’umma, kuma su ne gine-ginen hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka(Africa CDC) wadanda aka kammala gina su a kwanan baya, wadanda kuma suka mai da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka a matsayin daya daga cikin cibiyoyin kandagarkin cututtuka mafiya ci gaba da zamaninta a duniya. Kasar Sin ce ta samar da gudummawar gina shi, matakin da ya sa cibiyar ta zama ta biyu bayan cibiyar taron kungiyar tarayyar Afirka, wadda ita ma kasar Sin ce ta gina.

Afirka nahiya ce da aka fi samun kasashe masu tasowa, inda har yanzu ake fuskantar matsalolin kiwon lafiya, musamman ma sakamakon yaduwar annobar Covid-19, ya zama dole a gaggauta aikin gina tsarin kandagarkin cututtuka ta nahiyar. Yadda aka kammala aikin gina hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka a Afirka, babu shakka zai inganta karfin kasashen na kandagarkin cututtuka.

Mista Charles Onunaiju, masanin ilmin huldar kasa da kasa na Nijeriya, wanda kuma shi ne darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin a Nijeriya, yayin da ya tattauna da dan jarida a kwanan baya ya bayyana cewa, “Kasar Sin ta cika alkawarin da ta dauka na fara samar da kasashen Afirka rigakafin cutar Covid-19 da zarar ta kammala nazari da harhada rigakafin, ta kuma sanar da fara aikin gina cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka kafin lokacin da aka tsai da, ga shi kuma ta kammla aikin yadda ya kamata, kyaun alkawari cikawa, kuma duk wadannan sun shaida kasar Sin kasa ce mai rikon amana. Yanzu kuma ina da imanin cewa, batun gina al‘ummar Sin da Afirka mai Koshin lafiya ba batu ne na fatar Baki ba.”

ADVERTISEMENT

Daidai kamar yadda mista Onunaiju ya fada, tun bayan bullar cutar Covid-19 a Afirka a shekarar 2020, nan da nan kasar Sin ta samar da gudummawarta, kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya shugabanci taron hadin kan Sin da Afirka kan yaki da cutar Covid-19, inda ya gabatar da manufar nan ta gina al‘ummar Sin da Afirka mai koshin lafiya, kuma kawo yanzu, kasar Sin ta samar da rigakafi sama da miliyan 189 ga kasashen Afirka sama da 50, baya ga yadda ta yi kokarin aiwatar da hadin gwiwa da Masar da dai sauran kasashen Afirka, don kasashen su samu kwarewar samar da rigakafin da kansu. Ban da wannan, kasar Sin ta kuma tura tawagogin masana ilmin kiwon lafiya 5 da kuma kungiyoyin ma’aikatan lafiya 46 zuwa kasashen Afirka don su ba da taimako wajen dakile cutar a Afirka. Ga shi yanzu, kasar Sin ta kammala aikin gina hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka tare da mika ta hannun kungiyar tarayyar Afirka.

Daga wannan sabon mafari, muna fatan za a kara cimma sabbin ci gaba ta fannin ayyukan kiwon lafiya a kasashen Afirka bisa ga manufar nan ta gina al‘ummar Sin da Afirka mai koshin lafiya, don ta kasance laimar da ke kare al’ummomin kasashen Afirka daga cututtuka.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Sin da Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.