ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gina Al‘ummar Sin Da Afirka Mai Koshin Lafiya Ba Batu Ne Na Fatar Baki Ba 

by CMG Hausa
3 years ago
Sin da Afirka

A bayan garin birnin Addis Ababa na kasar Habasha, akwai jerin wasu gine-gine masu salo na musamman, wadanda suke matukar jan hankalin al’umma, kuma su ne gine-ginen hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka(Africa CDC) wadanda aka kammala gina su a kwanan baya, wadanda kuma suka mai da cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka a matsayin daya daga cikin cibiyoyin kandagarkin cututtuka mafiya ci gaba da zamaninta a duniya. Kasar Sin ce ta samar da gudummawar gina shi, matakin da ya sa cibiyar ta zama ta biyu bayan cibiyar taron kungiyar tarayyar Afirka, wadda ita ma kasar Sin ce ta gina.

Afirka nahiya ce da aka fi samun kasashe masu tasowa, inda har yanzu ake fuskantar matsalolin kiwon lafiya, musamman ma sakamakon yaduwar annobar Covid-19, ya zama dole a gaggauta aikin gina tsarin kandagarkin cututtuka ta nahiyar. Yadda aka kammala aikin gina hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka a Afirka, babu shakka zai inganta karfin kasashen na kandagarkin cututtuka.

Mista Charles Onunaiju, masanin ilmin huldar kasa da kasa na Nijeriya, wanda kuma shi ne darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin a Nijeriya, yayin da ya tattauna da dan jarida a kwanan baya ya bayyana cewa, “Kasar Sin ta cika alkawarin da ta dauka na fara samar da kasashen Afirka rigakafin cutar Covid-19 da zarar ta kammala nazari da harhada rigakafin, ta kuma sanar da fara aikin gina cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka kafin lokacin da aka tsai da, ga shi kuma ta kammla aikin yadda ya kamata, kyaun alkawari cikawa, kuma duk wadannan sun shaida kasar Sin kasa ce mai rikon amana. Yanzu kuma ina da imanin cewa, batun gina al‘ummar Sin da Afirka mai Koshin lafiya ba batu ne na fatar Baki ba.”

ADVERTISEMENT

Daidai kamar yadda mista Onunaiju ya fada, tun bayan bullar cutar Covid-19 a Afirka a shekarar 2020, nan da nan kasar Sin ta samar da gudummawarta, kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya shugabanci taron hadin kan Sin da Afirka kan yaki da cutar Covid-19, inda ya gabatar da manufar nan ta gina al‘ummar Sin da Afirka mai koshin lafiya, kuma kawo yanzu, kasar Sin ta samar da rigakafi sama da miliyan 189 ga kasashen Afirka sama da 50, baya ga yadda ta yi kokarin aiwatar da hadin gwiwa da Masar da dai sauran kasashen Afirka, don kasashen su samu kwarewar samar da rigakafin da kansu. Ban da wannan, kasar Sin ta kuma tura tawagogin masana ilmin kiwon lafiya 5 da kuma kungiyoyin ma’aikatan lafiya 46 zuwa kasashen Afirka don su ba da taimako wajen dakile cutar a Afirka. Ga shi yanzu, kasar Sin ta kammala aikin gina hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta Afirka tare da mika ta hannun kungiyar tarayyar Afirka.

Daga wannan sabon mafari, muna fatan za a kara cimma sabbin ci gaba ta fannin ayyukan kiwon lafiya a kasashen Afirka bisa ga manufar nan ta gina al‘ummar Sin da Afirka mai koshin lafiya, don ta kasance laimar da ke kare al’ummomin kasashen Afirka daga cututtuka.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Sin da Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Next Post
Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

Tabarbarewar Aikin Gwamnati A Matakin Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.