• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Zargi Masari Zai Kashe Miliyan 500 Don Tarbar Buhari A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Zargi Masari Zai Kashe Miliyan 500 Don Tarbar Buhari A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar adawa ta PDP a Jihar Katsina, ta zargi Gwamnan Jihar, Aminu Bello Masari, da bayar da umarnin kashe sama da Naira miliyan 500 daga asusun kananan hukumomin jihar don tarbar shugaban kasa Muhammadu Buhari zuwa jihar.

Ana sa ran Buhari zai kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu, daga ranar 26 zuwa 27 ga watan Janairu a jihar.

  • Limaman Masallatan Juma’a Na Arewa Sun Ayyana Goyon Bayansu Ga Takarar Tinubu Da Shettima 
  • Allah Ya Yi Wa Jarumin Kannywood, Abdulwahab Awarwasa Rasuwa

Sai dai jam’iyyar adawa ta PDP a jihar ta soki wannan shiri, inda ta alakanta da shi a matsayin almubazzaranci.

Shugaban kungiyar yada manufofin Atiku da Lado, Alhaji Lawal ÆŠan Ade ya yi zargin cewa za a kashe kudaden ba bisa ka’ida ba.

Alhaji Lawal Dan Ade, ne ya shaida wa manema labarai cikin wata takarda da ya ce gwamnan jihar, ya amince tare da sahale kashe kudaden.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

 

Masari
Alhaji Lawal Dan Ade

A cewarsa takardar wadda aka turawa Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar, ta nuna cewa za a cire miliyan N14,695,588.00 daga kowace karamar hukuma.

Adadin kudin da za a cire daga jihohin baki daya zai kai kimanin Naira miliyan N499,650,000.00

“Idan har wannan zargi da muke yi, ya tabbata muna kira da babbar murya cewa Katsinawa su fito su nuna rashin amincewarsu kan wannan badakala da aka shirya domin zuwan shugaba Buhari Jihar Katsina” in shi

Ya kuma kara da cewa ya kamata shugaba Buhari, ya nesanta kansa da wannan badakala da ake shirin aikatawa a jihar.

A cewarsa wadannan kudede akwai abubuwa da yawa da za a iya da su musamman wajen magance matsalolin da suka shafi makarantu da asibitoci da ‘yan gudun hijira da sauransu.

Sai dai Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na Jihar Katsina, Ya’u Umar Gwajo-gwajo, ya musanta wannan zargi, inda ya ce har yanzu idonsa bai ga wannan takarda da ake magana ba.

Kwamishinan ya sha alwashin bin diddigin wannan takarda da ake zargin an cire wadannan kudade.

Masari
Ya’u Umar Gwajo-gwajo

Ya ce zai bayyana abin da ake ciki game da maganar kudaden.

“Kamar yadda na fada cikin satin da ya gabata cewa kudaden kananan hukumomi suna nan ba gara ba zago, to har yanzu sunan nan, babu wata magana kan cewar za a cire wasu kudede domin zuwan shugaban kasa Jihar Katsina,” in ji shi.

Ana sa ran shugaba Buhari zai kai ziyarar ne don bude wasu manyan ayyuka da gwamnatin jihar ta yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKatsinaKudin Kananan HukumomiMasariTarbaZargiZiyarar Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Limaman Masallatan Juma’a Na Arewa Sun Ayyana Goyon Bayansu Ga Takarar Tinubu Da Shettima 

Next Post

Kasuwar Tafiye-Tafiyen Sin Ta Samu Farfadowa A Yayin Bikin Bazara 

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da É—umi-É—uminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 hour ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

13 hours ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

19 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da É—umi-É—uminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

23 hours ago
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

1 day ago
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

2 days ago
Next Post
Kasuwar Tafiye-Tafiyen Sin Ta Samu Farfadowa A Yayin Bikin Bazara 

Kasuwar Tafiye-Tafiyen Sin Ta Samu Farfadowa A Yayin Bikin Bazara 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.