ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Zargi Masari Zai Kashe Miliyan 500 Don Tarbar Buhari A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Masari

Jam’iyyar adawa ta PDP a Jihar Katsina, ta zargi Gwamnan Jihar, Aminu Bello Masari, da bayar da umarnin kashe sama da Naira miliyan 500 daga asusun kananan hukumomin jihar don tarbar shugaban kasa Muhammadu Buhari zuwa jihar.

Ana sa ran Buhari zai kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu, daga ranar 26 zuwa 27 ga watan Janairu a jihar.

  • Limaman Masallatan Juma’a Na Arewa Sun Ayyana Goyon Bayansu Ga Takarar Tinubu Da Shettima 
  • Allah Ya Yi Wa Jarumin Kannywood, Abdulwahab Awarwasa Rasuwa

Sai dai jam’iyyar adawa ta PDP a jihar ta soki wannan shiri, inda ta alakanta da shi a matsayin almubazzaranci.

ADVERTISEMENT

Shugaban kungiyar yada manufofin Atiku da Lado, Alhaji Lawal Ɗan Ade ya yi zargin cewa za a kashe kudaden ba bisa ka’ida ba.

Alhaji Lawal Dan Ade, ne ya shaida wa manema labarai cikin wata takarda da ya ce gwamnan jihar, ya amince tare da sahale kashe kudaden.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

 

Masari
Alhaji Lawal Dan Ade

A cewarsa takardar wadda aka turawa Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar, ta nuna cewa za a cire miliyan N14,695,588.00 daga kowace karamar hukuma.

Adadin kudin da za a cire daga jihohin baki daya zai kai kimanin Naira miliyan N499,650,000.00

“Idan har wannan zargi da muke yi, ya tabbata muna kira da babbar murya cewa Katsinawa su fito su nuna rashin amincewarsu kan wannan badakala da aka shirya domin zuwan shugaba Buhari Jihar Katsina” in shi

Ya kuma kara da cewa ya kamata shugaba Buhari, ya nesanta kansa da wannan badakala da ake shirin aikatawa a jihar.

A cewarsa wadannan kudede akwai abubuwa da yawa da za a iya da su musamman wajen magance matsalolin da suka shafi makarantu da asibitoci da ‘yan gudun hijira da sauransu.

Sai dai Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na Jihar Katsina, Ya’u Umar Gwajo-gwajo, ya musanta wannan zargi, inda ya ce har yanzu idonsa bai ga wannan takarda da ake magana ba.

Kwamishinan ya sha alwashin bin diddigin wannan takarda da ake zargin an cire wadannan kudade.

Masari
Ya’u Umar Gwajo-gwajo

Ya ce zai bayyana abin da ake ciki game da maganar kudaden.

“Kamar yadda na fada cikin satin da ya gabata cewa kudaden kananan hukumomi suna nan ba gara ba zago, to har yanzu sunan nan, babu wata magana kan cewar za a cire wasu kudede domin zuwan shugaban kasa Jihar Katsina,” in ji shi.

Ana sa ran shugaba Buhari zai kai ziyarar ne don bude wasu manyan ayyuka da gwamnatin jihar ta yi.

Masari
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Kasuwar Tafiye-Tafiyen Sin Ta Samu Farfadowa A Yayin Bikin Bazara 

Kasuwar Tafiye-Tafiyen Sin Ta Samu Farfadowa A Yayin Bikin Bazara 

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.