• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Machina Ya Yi Barazanar Daukar Matakin Shari’a Kan Sauya Sunansa Da Ahmad Lawan

by Muhammad
3 years ago
Machina

Dan takarar kujerar Sanata a karkashin jam’iyyar APC mai wakiltar Yobe ta Arewa a jihar Yobe, Hon. Bashir Sheriff Machina, ya yi barazanar shigar da kara kan zargin sauya sunansa da na shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, a cikin jerin sunayen da jam’iyyar ta aike wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a ranar Juma’a.

Jam’iyyar APC da wasu ‘yan takarar sanata a fadin jihohi 36 na tarayya da babban birnin tarayya (FCT) ne suka sanya sunan Lawan a cikin sunan da aka aike wa hukumar.

  • Lawan Na Fuskantar Barazanar Rasa Kujerarsa Wanda Ya Maye Gurbinsa Ya Ki Janye Masa
  • Abun Mamaki: Lawan ya Manta Da Wasikar Murabus Din Abaribe A Gida

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Machina ya tsaya takara a zaben fidda gwani na jihar Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC a zaben fiida gwani da INEC da hukumomin tsaro suka sanyawa hannu.

Amma Lawan, wanda ya tsaya takarar shugaban kasa a jam’iyyar kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu bai shiga zaben fidda gwani na takarar Sanata na jam’iyyar a yankin Yobe ta Arewa ba.

Sai dai APC ta rubuta wa INEC wasika, inda ta sanar da hukumar zaben cewa shugaban majalisar dattawa ne zai tsaya mata takarar kujerar sanatan Yobe ta Arewa, wadda Lawan ke wakilta a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Machina ya mayar da martani ga wannan matakin na Jam’iyya a daren Juma’a, kuma ya sha alwashin garzaya kotu domin kalubalantar yunkurin kwace masa hakkinsa.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, Machina ya roki jam’iyyar APC da ta gyara sunansa, inda ya ce ba shi da wani zabi da ya wuce ya nemi a yi masa shari’a idan aka maye gurbinsa da na Lawan.

Machina, ya shan alwashin ba zai ja da baya kan wannan kudurin ba, ya ce, “A cikin jerin sunayen da aka aika wa INEC, an gano ba sunana bane. Ban sani ba ko kuskure ne, sunana ba ya cikin jerin sunayen da aka ce za a gabatar a yau ga INEC. Don ni ne dan takarar da aka zaba na jam’iyyar APC ta shiyyar Yobe ta Arewa a majalisar dattawa.

“Ni ne zababben dan takara; Ban janye wa kowa ba, kuma ba zan janye ba, domin a matsayin hakki na wannan yake, shi ne aikin da ‘yan jam’iyyarmu da wakilai suka ba ni. Don haka cire sunana cikin sirri, rashin bin tsarin demokradiyya ne.

“Insha Allahu zan dauki matakai, na farko ta hanyar tunatarwa da kuma kira ga jam’iyyata cewa idan har da gaske aka yi wannan mataki a gyara, musamman idan aka yi kuskure. A gaskiya muna neman gyara daga kwamitin ayyuka na jam’iyyarmu ta kasa a karkashin jagorancin Sanata Abdullahi Adamu, cewa akwai wata matsala kuma muna bukatar a gyara.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.