ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Machina Ya Yi Barazanar Daukar Matakin Shari’a Kan Sauya Sunansa Da Ahmad Lawan

by Muhammad
4 years ago
Machina

Dan takarar kujerar Sanata a karkashin jam’iyyar APC mai wakiltar Yobe ta Arewa a jihar Yobe, Hon. Bashir Sheriff Machina, ya yi barazanar shigar da kara kan zargin sauya sunansa da na shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, a cikin jerin sunayen da jam’iyyar ta aike wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a ranar Juma’a.

Jam’iyyar APC da wasu ‘yan takarar sanata a fadin jihohi 36 na tarayya da babban birnin tarayya (FCT) ne suka sanya sunan Lawan a cikin sunan da aka aike wa hukumar.

  • Lawan Na Fuskantar Barazanar Rasa Kujerarsa Wanda Ya Maye Gurbinsa Ya Ki Janye Masa
  • Abun Mamaki: Lawan ya Manta Da Wasikar Murabus Din Abaribe A Gida

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Machina ya tsaya takara a zaben fidda gwani na jihar Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC a zaben fiida gwani da INEC da hukumomin tsaro suka sanyawa hannu.

ADVERTISEMENT

Amma Lawan, wanda ya tsaya takarar shugaban kasa a jam’iyyar kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu bai shiga zaben fidda gwani na takarar Sanata na jam’iyyar a yankin Yobe ta Arewa ba.

Sai dai APC ta rubuta wa INEC wasika, inda ta sanar da hukumar zaben cewa shugaban majalisar dattawa ne zai tsaya mata takarar kujerar sanatan Yobe ta Arewa, wadda Lawan ke wakilta a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Machina ya mayar da martani ga wannan matakin na Jam’iyya a daren Juma’a, kuma ya sha alwashin garzaya kotu domin kalubalantar yunkurin kwace masa hakkinsa.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, Machina ya roki jam’iyyar APC da ta gyara sunansa, inda ya ce ba shi da wani zabi da ya wuce ya nemi a yi masa shari’a idan aka maye gurbinsa da na Lawan.

Machina, ya shan alwashin ba zai ja da baya kan wannan kudurin ba, ya ce, “A cikin jerin sunayen da aka aika wa INEC, an gano ba sunana bane. Ban sani ba ko kuskure ne, sunana ba ya cikin jerin sunayen da aka ce za a gabatar a yau ga INEC. Don ni ne dan takarar da aka zaba na jam’iyyar APC ta shiyyar Yobe ta Arewa a majalisar dattawa.

“Ni ne zababben dan takara; Ban janye wa kowa ba, kuma ba zan janye ba, domin a matsayin hakki na wannan yake, shi ne aikin da ‘yan jam’iyyarmu da wakilai suka ba ni. Don haka cire sunana cikin sirri, rashin bin tsarin demokradiyya ne.

“Insha Allahu zan dauki matakai, na farko ta hanyar tunatarwa da kuma kira ga jam’iyyata cewa idan har da gaske aka yi wannan mataki a gyara, musamman idan aka yi kuskure. A gaskiya muna neman gyara daga kwamitin ayyuka na jam’iyyarmu ta kasa a karkashin jagorancin Sanata Abdullahi Adamu, cewa akwai wata matsala kuma muna bukatar a gyara.”

Machina
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.