ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Machina Ya Yi Barazanar Daukar Matakin Shari’a Kan Sauya Sunansa Da Ahmad Lawan

by Muhammad
4 years ago
Machina

Dan takarar kujerar Sanata a karkashin jam’iyyar APC mai wakiltar Yobe ta Arewa a jihar Yobe, Hon. Bashir Sheriff Machina, ya yi barazanar shigar da kara kan zargin sauya sunansa da na shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, a cikin jerin sunayen da jam’iyyar ta aike wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a ranar Juma’a.

Jam’iyyar APC da wasu ‘yan takarar sanata a fadin jihohi 36 na tarayya da babban birnin tarayya (FCT) ne suka sanya sunan Lawan a cikin sunan da aka aike wa hukumar.

  • Lawan Na Fuskantar Barazanar Rasa Kujerarsa Wanda Ya Maye Gurbinsa Ya Ki Janye Masa
  • Abun Mamaki: Lawan ya Manta Da Wasikar Murabus Din Abaribe A Gida

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, Machina ya tsaya takara a zaben fidda gwani na jihar Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC a zaben fiida gwani da INEC da hukumomin tsaro suka sanyawa hannu.

ADVERTISEMENT

Amma Lawan, wanda ya tsaya takarar shugaban kasa a jam’iyyar kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu bai shiga zaben fidda gwani na takarar Sanata na jam’iyyar a yankin Yobe ta Arewa ba.

Sai dai APC ta rubuta wa INEC wasika, inda ta sanar da hukumar zaben cewa shugaban majalisar dattawa ne zai tsaya mata takarar kujerar sanatan Yobe ta Arewa, wadda Lawan ke wakilta a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Machina ya mayar da martani ga wannan matakin na Jam’iyya a daren Juma’a, kuma ya sha alwashin garzaya kotu domin kalubalantar yunkurin kwace masa hakkinsa.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, Machina ya roki jam’iyyar APC da ta gyara sunansa, inda ya ce ba shi da wani zabi da ya wuce ya nemi a yi masa shari’a idan aka maye gurbinsa da na Lawan.

Machina, ya shan alwashin ba zai ja da baya kan wannan kudurin ba, ya ce, “A cikin jerin sunayen da aka aika wa INEC, an gano ba sunana bane. Ban sani ba ko kuskure ne, sunana ba ya cikin jerin sunayen da aka ce za a gabatar a yau ga INEC. Don ni ne dan takarar da aka zaba na jam’iyyar APC ta shiyyar Yobe ta Arewa a majalisar dattawa.

“Ni ne zababben dan takara; Ban janye wa kowa ba, kuma ba zan janye ba, domin a matsayin hakki na wannan yake, shi ne aikin da ‘yan jam’iyyarmu da wakilai suka ba ni. Don haka cire sunana cikin sirri, rashin bin tsarin demokradiyya ne.

“Insha Allahu zan dauki matakai, na farko ta hanyar tunatarwa da kuma kira ga jam’iyyata cewa idan har da gaske aka yi wannan mataki a gyara, musamman idan aka yi kuskure. A gaskiya muna neman gyara daga kwamitin ayyuka na jam’iyyarmu ta kasa a karkashin jagorancin Sanata Abdullahi Adamu, cewa akwai wata matsala kuma muna bukatar a gyara.”

Machina
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

A Bana Ne Sin Ta Samu Sakamako Mai Kyau Wajen Sa Kaimi Ga Yin Hadin Gwiwa A Tsakanin Kasashen BRICS

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.