• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadimar Tambuwal Ta Rasu Sakamakon Turmutsutsu A Wajen Taron PDP A Sakkwato

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Hadimar Tambuwal Ta Rasu Sakamakon Turmutsutsu A Wajen Taron PDP A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakiya ta musamman ga Gwamna Aminu Waziri Tambuwal kan harkokin Ilimin mata, Hajiya Aishat Maina ta rasu.

Ta rasu ne bayan halartar taron gangamin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP da ya gudana a Jihar Sakkwato a ranar Talata.

  • Sin Na Tsayawa Tsayin Daka Kan Yaki Da Ta’addanci
  • Da Dumi-Dumi: Mahara Sun Kashe DPO Da Wasu A Benue

Leadership Hausa ta gano cewa, ta shiga cikin turmutsitsin da ya afku a kofar fitta daga filin taron.

“Wani direban babur ne ya fado daga kan babur dinsa a hanyar fita dava filin wanda hakan ya haifar da mumunan turmutsutsu, inda mutane suka fado kan juna. Tana daya daga cikin wadanda abin ya shafa,” cewar wata majiya.

Da yake tabbatar da hakan, shugaban kungiyar masu ba da shawara na musamman, Ibrahim Magaji Gusau, ya ce an ceto marigayiyar, inda aka garzaya da ita Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato domin yi mata magani.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

“Abun takaici ta mutu ‘yan mintuna kadan bayan kai ta asibiti,” in ji shi Magaji, wanda ya bayyana ta a matsayin mai kwazo da hazaka.

“Ko a lokacin taron, muna tare, ba tare da sanin cewa hakan zai zama taronmu na karshe ba,” in ji shi, ya yi mata addu’ar Allah ya gafarta mata kurakuranta, ya kuma sanya ta a Jannatul Firdaus.

Marigayiyar dai tsohuwar shugabar kungiyar ‘yan jarida ce ta kasa (NAWOJ) a Jihar Sakkwato.

Ta kuma kasance tsohuwar mai bai wa Gwamna Aminu Tambuwal shawara kan sabbin kafafen yada labarai kafin a dauke ta zuwa Hukumar Ilimi ta Mata.

Tsohon Shugaban Kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ) a Jihar Sakkwato, Isa Abubakar Shuni, ya bayyana kaduwarsa bisa rasuwar ‘yar jaridar ba zato ba tsammani, inda ya bayyana cewa ta ba da gudunmawa sosai ga harkar aikin jarida a jihar.

Ta rasu ta bar ‘ya’ya uku da kuma iyayenta tsofaffi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HadimaRasuwaSakkwatoTambuwalTaron PDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Marwa Ya Sadaukar Da Karramawar LEADERSHIP Ga Buhari Da Jami’an NDLEA

Next Post

Ina Ci Gaba Da Tattaunawa Da Kwankwaso Da Obi Kan Mara Min Baya – Atiku 

Related

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

8 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

13 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

19 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

1 day ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

2 days ago
Next Post
Ina Ci Gaba Da Tattaunawa Da Kwankwaso Da Obi Kan Mara Min Baya – Atiku 

Ina Ci Gaba Da Tattaunawa Da Kwankwaso Da Obi Kan Mara Min Baya - Atiku 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.