• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Atiku Ya Nemi Afuwar ‘Yan Nijeriya – Sanata Adeyemi

by Sadiq
3 years ago
Adeyemi

Sanata Smart Adeyemi, ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da ya roki gafarar ‘yan Nijeriya maimakon neman kujerar shugaban kasa.

Adeyemi, wanda ke wakiltar Kogi ta Yamma a Majalisar Dokoki, ya bayyana haka ne a lokacin da yake tattaunawa da ’yan asalin Jihar Kogi mazauna Minna a ranar Talata a wani taron mara wa Tinubu da Shettima baya.

  • Cikin Shekaru 3 Da Suka Gabata Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Yaki Da Annobar COVID-19 
  • Emefiele Ya Bayyana A Gaban Majalisa Kan Sauya Fasalin Kudi

Ya ce ya kamata tsohon mataimakin shugaban kasar ya nemi afuwar ‘yan Nijeriya kan sayar da dukiyar kasa baki daya.

“Atiku karkashin kulawarsa a matsayinsa na shugaban kamfanonin kasuwanci, ya sayar da dukiyoyinmu na gama-gari, kuma shi ne tushen talauci da rashin tsaro a Nijeriya.

“Don haka Atiku ya kamata ya fara bai wa ‘yan Nijeriya hakuri kan yadda suka kashe Naira biliyan 16 don samar da wutar lantarki amma ba mu da wutar lantarki ta sa’o’i 24.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

“Ya kamata Atiku ya bayyana mana irin yadda suka karkatar da dukiyar gwamnati wanda ko shakka babu ya hada da rashin tsaro da tattalin arzikin Nijeriya a yau sakamakon aika-aikar da PDP ta yi wanda Atiku Abubakar ya jagoranta,” in ji shi.

Sai dai Sanatan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su marawa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da Kashim Shettima baya ya kara da cewa dukkansu mutane ne masu gaskiya.

“Abin da Nijeriya ke bukata a yanzu shi ne mutum mai hangen nesa ta yadda za a inganta rayuwarmu, ta yadda za mu ci moriyar tsaron rayuka da dukiyoyi da kuma tattalin arzikin kasar nan ya kai wani matsayi mai girma,” in ji shi.

Ya bayyana Tinubu da Shettima a matsayin wani babban hadin kai.

A nasa jawabin, Gwamna Abubakar Sani-Bello na Jihar Neja, ya yi tir da halin da kasar nan ke ciki idan ya kwatanta shi da yadda ta kasance kafin shekarar 1999, ya kuma shawarci ‘yan Nijeriya da su zabi shugabannin da suka cancanta da za su fitar da kasar nan daga halin da ta ke ciki.

“Halin da Nijeriya ke ciki kafin 1999 da abin da yake faruwa a yanzu ya sa na koka kan makomar ‘ya’yanmu.

“Amma yanayin da muke ciki a yau abun bakin ciki ne kuma abin da Nijeriya ta kasance a yau yana da matukar tausayi,” in ji shi.

Bello ya yaba wa al’ummar Kogi mazauna jihar tare da yin kira a gare su da sauran wadanda ba ‘yan asalin jihar ba da su mara wa jam’iyyar APC baya su zabi duk ‘yan takararta.

A nasa jawabin, Sarkin Ebira a Neja, Alhaji Mansu Abdul, ya yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya ga dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC a matakin jiha da kasa baki daya.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya rawaito cewa taron ya kuma shaida rabon kayan aiki ga mutanen Kogi mazauna Neja.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

October 22, 2025
Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi
Manyan Labarai

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano

'Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.