• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Uwargida Za Ta Yi Da Mijin Da Bai Iya Zaman Hira Ba?

by Amina Usman
2 years ago
in Al'adu
0
Wata Mata Ta Yi Wuf Ta Aure Saurayin Diyarta A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidan aure gida ne na zama har abada, zama ne da aka faro shi a sanadin soyayya. Zaman gidan aure zama ne da ke bukatar nuna kulawa ba da lokaci da kuma sadaukarwa.

Duk wadannan abubuwan suna samuwa ne ta hanyar hadin kai da uwargida da kuma shi kanshi Mijin. Zaman aure zama ne da ke bukatar lokaci, to in akasin haka ya faru ya uwargida za ta tunkari wannan matsala? To a gaskiya fuskantar wannan yanayi dole sai Uwargida ta hada da dabaru iri daban-daban.

  • Ya Uwargida Za Ta Yi Mu’amula Da Uwar Mijin Da Zama Ya Hada Su?

Idan uwargida Allah ya hada ta da mijin da bai iya zaman hira ba to fa akwai wasu halayya da dabi’u da za ta koya saboda samun zama mai dorewa. Akwai hanyoyi da dama da uwargida za ta bi domin shawo irin wannan matsalar.

Abu na farko shi ne uwargida dole ta zama mai hakuri domin kuwa abin da hakuri bai ba da ba rashin shi ba zai ba da ba. Idan uwargida ta fahimci mijinta mutum ne da bai iya zaman hira da mace ba to abin da za ta fara yi shi ne daga ya dawo gida ya zauna da ma Uwargida ta tabbatar da ta tanadi labarai da za ta yi wa maigida wanda suka hada da na nishadi da kuma na ban al’ajabi,
Idan uwargida na son hira da miji ba fa daga dawowansa za ki sake ki fara zuba ba, ki karanci yanayin fuskar sa tukunna in yana cikin walwala to da ma labarai da za ki bayar su kasance na nishadi da barkwanci in kuma ta ga yanayinsa na rashin jin dadi ne to labarai ta za su kasance na tausayi da kuma darussan zaman duniya.

Kar uwargida ta ce kullum ita kadai take abu daya ta gaji, haka nan za ki daure ki ci gaba dama ai ibada akwai wahala saboda haka uwargida ta dauka wani jihadi ne za ta yi.

Labarai Masu Nasaba

GORON JUMA’A 28-03-2025

GORON JUMA’A 14-02-2025

Sannu a hankali uwargida za ta cimma riban abin da take nema. Da yawa gidan aure rashin hira shi ke haddasa rashin jituwa a tsakanin uwargida da maigida saboda hira abu ne da ke kara shakuwa da soyayya a tsakanin ma’aurata.

Yawanci sai ka ga gidaje ana zaman ko in kula tsakanin uwargida da maigida ya dawo aiki ya shige daki ke kuma uwargida kin hakimce a falo kin sa Talabijin a gaba kina kallo, to ba haka ake yi ba ko da a ce ba mai son hira ba ne mijinki, bi shi ki karanci yanayinsa, kirkiro tadi da haka tun kina yi ba ya ansawa har ya zo ya fara ansawa gaba-gaba sai ki ga da kanshi ya fara bude baki yana magana, sai dai fa uwargida ba za ta cimma wannan nasara ba har sai ta hada da kalmar nan da ta dade tana ji wato’ HAKURi’.

Rashin zaman hira da miji yana haddasa rashin jituwa ko dan yaya ne, uwargida ta daure ta dinga jefo magana daya tare da amfani da ilmin kissa da Allah ya ba ta tana yi, tana yi har ta cimma nasara ya fara tanka mata.

Shi fa namiji kamar karamin yaro yake, yadda kika masa tarbiyya haka za ku tafi da shi, in kika masa daya kafin a kai ga na biyu zai amsa miki, kar ki ce kin gaji, daure ki jajirce saboda akwai mijin da shi fa bai iya hira ba, bai san ta ina zai fara ba amma in kika fara dago masa sai ki ga kun ja awanni kuna tadawa. Hira da miji kan sa uwargida ta fahimci ina suka dosa a zaman auren su.

Na san da yawa mata za su ce su fa sun gaji ba za su iya suna magana ana amsa musu da eh ko a’a ba, kar ki gaji, wannan amsawar da yake yi za ki ga ribarta wata rana saboda duk ranar da kika yi shiru sai ya ji ba dadi saboda ya saba sai ki ga daga nan ya bude bakinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin ‘Yan Bindiga: Adadin Mutanen Da Aka Kashe Ya Karu Sama Da Mutum 100 A Katsina

Next Post

Sauya Takardun Kuɗi: Jam’iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023

Related

GORON JUMA’A
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 28-03-2025

2 months ago
GORON JUMA’A
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 14-02-2025

3 months ago
GORON JUMA’A 12-12-2024
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 9-01-2025

4 months ago
GORON JUMA’A 12-12-2024
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 3-01-2025

4 months ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

4 months ago
GORON JUMA’A 12-12-2024
Goron Juma'a

GORON JUMA’A 12-12-2024

5 months ago
Next Post
Sauya Takardun Kuɗi: Jam’iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023

Sauya Takardun Kuɗi: Jam'iyyu Siyasa 13 A Nijeriya Sun Yi Barazanar Ƙaurace Wa Zaɓen 2023

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

May 12, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.