ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Uwargida Za Ta Yi Mu’amula Da Uwar Mijin Da Zama Ya Hada Su?

by Amina Usman
3 years ago
Pensive African American young woman look in distance thinking pondering, thoughtful biracial millennial female lost in thoughts, suffer from depression or miscarriage, psychological help concept

Pensive African American young woman look in distance thinking pondering, thoughtful biracial millennial female lost in thoughts, suffer from depression or miscarriage, psychological help concept

Zamantakewa mu’amula ce da ke faruwa tsakanin mutane daban-daban. In aka ce zama ya hada ka da mutum to fa dole ka kasance mai abu biyu, Hakuri da Kauda kai.

Zama na aure zama ne da yake kunshe da kalubale mai dadi ko akasin haka, musamman in aka ce zama ya hada ka da uwa ko kuma wani dangi na miji. Da yawa mata suna daukan zama da uwar miji a matsayin wani zama mai tattara da kalubale wanda abun ba haka yake ba.

  • Cutar Shakewar Numfashi Ta Kashe Mutum 25 A Jihar Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Raunata Wasu A Katsina

Idan uwargida ta tsinci kanta a cikin matan da zama da uwar miji ya hada su to fa dole sai kin karo biyayya a kan wanda kike da shi, in aka ce biyayya ina nufin yanda uwargida za ta kalli mahaifanta haka ya kamata ta girmama na mijinta, yadda za ta yiwa iyayenta ladabi to su ma fa haka za ta yi musu.

ADVERTISEMENT

Sannan uwargida ta kasance mai ihsani da kyautatawa tsakanin ta da uwar miji, idan uwar mijin na cin goro ta lazamci siya ta bata. Haka turare na jiki da na daki shi ma ta dan dinga siya tana ba ta ko ba kullum ba ko a wata sau daya.

Uwargida kar ki taba yarda ku raba tukunya da uwar mijinki, saboda yin haka yana kawo rabuwan kai sosai, in dai zaman gida ya hada uwsargida da sirika to ki daure ki kasance kina dafa abinci duka gida kuma kar ki kasance mai rowa ki zuba mata adadin da kika san zai ishe ta har ma wani bako ya zo ya ci, saboda yin hakan yana kara wa uwargida daraja da kima a idon sirikar ta da ma idon duniya baki daya. Kuma ko zaginta uwar mijin ta ji ana yi za ta so ta kare ta.

LABARAI MASU NASABA

Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?

Sharrin Da Ke Tattare Da Jifan Iyali Da Munanan Kalamai

Uwargida ta kasance mai kauda kai ga abinda surukarta za ta yi ko ta ki yi. Kar uwargida ta ga an yi baki sun shige daki ta kwallafa rai sai ta kasa kunne ta ji me ake fada, ko kila tadinta ake yi, kar ki sake kiyi wannan za ki jiyo wa kanki abin da zai hana ki kwanciyar hankali, tun farko ma uwargida kar ta sa wa ranta wannan, ta sa wa zuciyar ta salama, ta sa wa ranta cewa in an yi baki a gidan to abin da ya dame su suke zantawa.

Kar uwargida ta kasance mai sa ido ga abinda Mijinta ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kasance mai kauda kai domin kuwa hakan zai kara mata daraja da kima a idon shi. Duk abin da zai kawo kar ki ce ke ma fa dole sai an miki a’a ki kauda kai in akwai rabonki sai ki ga ke ma an kawo miki. Kuma yin hakan yana kara wa uwargida daraja da kima a idon kowa ma ba miji kadai ba.

Aikace-Aikacen gida kar uwargida ta dauka zaman uwar mijinta a kusa da ita wata dama ce da za ta dinga saka uwar miji aiki ko kadan hakan ba tarbiyya ba ce kuma babu dan da zai ga haka ya ji dadi. Ko da ita ta nemi ta tayaki ki nuna mata ita uwa ce lokacin hutunta ne saboda haka ta je ta huta za ki yi aikin.

Nuna wa Maigida ya kyautata wa uwarsa kar uwargida ta jira wai sai dole miji ya yi wa uwarsa a’a ke ma kamar idonsa kike a gidan saboda haka ki nuna masa duk wasu hanyoyin kyautata wa mahaifiya, ki dinga nuna masa wanda hakan zai kara miki kima da daraja sosai a idonsa.

Uwar Miji
Amina Usman
+ postsBio
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Gasasshen Nama Mai Dankali
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Shawara Ga Ma’aurata Game Da Hassada
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Yadda Ake Miyar Zogale
  • Amina Usman
    https://hausa.leadership.ng/author/amina-usman/
    Amfanin Danyen Kwai Wajen Magance Kurajen Fuska

MASU ALAKA

Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
Zamantakewa

Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?

May 31, 2026
Uwar Miji
Taskira

Sharrin Da Ke Tattare Da Jifan Iyali Da Munanan Kalamai

May 10, 2026
Ra’ayin Matasa Game Da Auren Kusa Da Na Nesa
Labarai

Ra’ayin Matasa Game Da Auren Kusa Da Na Nesa

April 19, 2026
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

Gwamnatin Bauchi Ta Fayyace Zare Da Abawa Kan Filin Makabarta A Yolan Bayara

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.