Dandazon jama’a da dama sun taru don gudanar da zanga-zangar lumana a kan babbar hanyar Ore-Benin a Jihar Ondo, don nuna rashin jin dadinsu kan rashin kudi da kuma karancin man fetur.
Masu zanga-zangar da suka fusata sun tare hanyar wanda hakan ya haifar da cunkoson ababen hawa.
- Duniya Ta Shiga Alhinin Mutuwar Sama Da Mutum 3,000 A Turkiyya Da Siriya
- Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso
Matafiya da dama da ke bin hanyar sun makale na sa’o’i da dama.
Daya daga cikin masu zanga-zangar, Adebayo Adeyemi, ya ce wahalhalun da ‘yan Nijeriya ke fuskanta a baya-bayan nan a fadin kasar nan abin ban tsoro ne.
“Muna zanga-zangar ne don aika sako ga gwamnati, cewa mu talakawa muna shan wahala,” in ji Adeyemi.
Cikakken bayani na tafe…
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp