• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Bude Wa Tawagar Jami’an Tsaron Okowa Wuta Sun Kashe ‘Yansanda Uku

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Bude Wa Tawagar Jami’an Tsaron Okowa Wuta Sun Kashe ‘Yansanda Uku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan sanda uku sun mutu lokacin da wasu ‘yan bindiga suka yi wa tawagar jami’an tsaron gwamnan Ifeanyi Okowa na jihar Delta kwanton bauna.

Lamarin ya faru ranar Juma’ar nan da misalin karfe 1:30 na rana.

  • Atiku Da Okowa Sun Janye Daga Taron Ganawa Da ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
  • Okowa Ya Karbi Wadanda Suka Nemi Takarar Gwamnan APC Uku Da Suka Koma PDP A Sakkwato 

Okowa shi ne mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP.

Jaridar Premium Times ta rawaito cewa ‘yan bindigar sun kai wa tawagar jami’an tsaro hari wadanda suka hada da ‘yan sanda hudu a unguwar Ihiala, da ke karamar hukumar Ihiala ta jihar Anambra, a yankin kudu maso gabashin Nijeriya.

Sai dai an ce wai ‘yan bindigar sun sako daya daga cikin jami’an da ba ya cikin kakin ‘yan sanda a yayin harin.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Wasu majiyoyi sun ce jami’an na kan hanyar zuwa jihar Abia ne, inda Okowa zai je don ganawa da wasu ‘ya’yan jam’iyyar PDP a jihar gabanin zaben shugaban kasa da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Kawo yanzu dai ba a bayyana ko Okowa na tafiya tare da jami’an ba a yayin kai harin ba.

Jami’an da aka kashe sun hada da Celestine Nwadiokwu da Jude Obuh da kuma Lucky Aleh.

Lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, Tochukwu Ikenga a safiyar ranar Asabar, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ikenga, ya ce wadanda harin ya rutsa da su jami’an su ne da ke aiki a sashin kula da bama-bamai na rundunar ‘yan sandan jihar Delta kuma suna bakin aikin lamarin ya faru.

Kakakin ‘yan sandan ya ce rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta gano gawarwakin jami’an uku da aka kashe bayan samun labarin kai harin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaAnambraAtikuDeltaKasheKisaOkowa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jerin ‘Yan Wasan Da Kwantiranginsu Zai Kare A Karshen Kakar Bana

Next Post

Mahaukaci Kadai Ne Zai Iya Sake Zaben APC – Ayu

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

1 hour ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

3 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

18 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

18 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

19 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

19 hours ago
Next Post
Mahaukaci Kadai Ne Zai Iya Sake Zaben APC – Ayu

Mahaukaci Kadai Ne Zai Iya Sake Zaben APC – Ayu

LABARAI MASU NASABA

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.