ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahaukaci Kadai Ne Zai Iya Sake Zaben APC – Ayu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Ayu

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Dakta Iyorchia Ayu ya bayyana cewa ma-haukaci kadai ne zai iya sake zaben jam’iyyar APC duba da irin bakar wahalar da ‘yan Nijeriya suka shiga na tsawon shekaru takwas na mulkin APC.

Ayu ya bayyana hakan ne a Jihar Benuwai lokacin gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na PDP, inda ya bukaci mutane su zabi duka ‘yan takarar jam’iyyarsa.

  • PDP Ta Kori Nnamani, Ogbu, Dan Fayose, Da Wasu Daga Jam’iyyar

Ya ce PDP ta magance matsalar gwamnan Jihar Abiya, Okezie Ikpeazu, sannan suna kokarin lallashin fusatattun gwamnonin PDP guda biyar wadanda suka bijire.

ADVERTISEMENT

Ya ce wannan shi ne dan takarar shugaban kasa daya tilo na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar wanda ya yi alkawarin idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasa zai dawo da zaman lafiya a wannan jiha da kuma sake bude tashar jirgin kasa da ke jihar.

Haka kuma Ayu ya ce duk da cewa akwai korafe-korafe a cikin babbar jam’iyyar adawa, ya dage da cewa jam’iyyar ba ta rabu ba, yana mai jaddada cewa tuni jam’iyyar ta fara tattaunawa da dukkan ‘ya’yanta da suka fusata domin ganin sun dawo cikin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Abin da dukkaninmu muka sani shi ne, ana shan wahala a kasar nan a cikin she-karu takwas da APC ta shafe a kan mulki, wanda ke da matsalar tabin hankali ne kwai zai sake zaben APC. Kar ku kuskura ku bata kuri’unku.

“Ku zabi kowane dan takarar PDP, jam’iyyar ba ta rabu ba. Akwai mambobi kali-lan da suka fusata kuma muna magana da su. Za mu tabbatar sun dawo cikin jam’iyyar domin mu yi aiki tare gaba daya. Mako daya ya isa a sauya komi. Dama hakan yana faruwa kuma ina tabbatar da cewa za mu karbi kowa da kowa,” in ji shi.

Ya roki gwamnan Jihar Benuwai, Samuel Ortom ya dawo domin yakin ceto Nijeri-ya daga hannun APC.

Ortom yana daga cikin mambobin gwamnonin PDP na G-5, tawagar fusatattun gwamnonin guda biyar na jam’iyyar wanda gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike yake jagoranta da ke neman sai Ayu ya sauka daga mukaminsa a matsayin sharad-in yin sulhu.

Sauran mambobin na G5 sun hada da gwamnan Jihar Inugu, Ifeanyi Ugwanyi da gwamnan Jihar Abiya, Okezie Ikpeazu da kuma gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde.

Ayu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Ayu
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Ba Mu Da Takardun Kuɗi Da Zamu Buga Sababbin Kuɗi Isassu Su Wadata – Emefiele

Ba Mu Da Takardun Kuɗi Da Zamu Buga Sababbin Kuɗi Isassu Su Wadata – Emefiele

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.