• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEF Ga Buhari: Kar Ka Sake A Karkashin Mulkinka Ka Bari IPOB Ta Hana ‘Yan NIjeriya Kada Kuri’a

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
NEF Ga Buhari: Kar Ka Sake A Karkashin Mulkinka Ka Bari IPOB Ta Hana ‘Yan NIjeriya Kada Kuri’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar dattawan Arewa (NEF) ta yi kira ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari da kar ya sake a karkashin mulkinsa ya bari wata kungiya, musamman kungiyar neman kafa kasar Biafara (IPOB) ta hana ‘yan Nijeriya yin zabe.

A cikin sanarwar da mai magana da yawun kungiyar, Dakta Hakeem Baba-Ahmed ya fitar a ranar Talata, kungiyar ta yi Allah wadai da yadda IPOB ke barazana ga zaben 2023 a yankin kudu maso gabashin Nijeriya.

  • Za A Kira Taruka Biyu A Farkon Wata Mai Zuwa
  • Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

Kungiyar ta koka da yadda shuwagabanni, dattijai da ‘yan siyasa daga yankin da sauran sassan Nijeriya suka yi gum da bakunansu kan wannan barazana mai hatsari, wanda ta ce yana da matukar tayar da hankali.

Kungiyar ta jaddada cewa ‘yan NIjeriya na son a gudanar da sahihin zabe da kuma mika mulki cikin lumana zuwa gwamnati mai zuwa, inda ta ce babu wata kungiya da za a bari ta jefa al’ummar kasar cikin mawuyacin hali ta hanyar barazana ga zabe da zaman lafiya a kasar nan.

Ta ce: “Wadannan barazanar na biyo bayan hare-haren da ake kai wa gine-ginen gwamnati da kashe-kashe, ciki har da kashe ‘yansanda a yankin. Idan har ba a dauki matakan da suka dace ba, wadanda ke gudanar da ayyukan rashin bin doka suna iya dauka cewa za su yi nasara.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

“Duk wani yunkuri na yin katsalandan a ‘yancin ‘yan Nijeriya na shiga hurumin hana su zaben shugabanninsu, babban hari ne ga diyaucin Nijeriya kuma matakin da ya kamata a bijire masa ne.”

A cewar kungiyar, barazana ga zabuka babbar barazana ce ga tsarin dimokuradiyya da kuma ginshikin da al’ummar kasar suka dogara a kai, inda ta kara da cewa, idan har ta samu nasara, barazanar za ta nuna cewa za a fara wasu rikice-rikicen da kasar za ta kasa farfadowa.

“Kungiyar tana kira ga gwamnatin Shugaba Buhari da ta tabbatar da halaccin ikonta a kan duk wata kungiyar da ba ta da doka a kowane sashe na kasar nan tare da tabbatar da cewa ba a hana masu kada kuri’a ko barazana ba.”

Haka kuma, ta lura cewa dole ne shugabanni su fito fili su yi Allah wadai da wannan munanan barazanar tare da tabbatar wa ‘yan kasa masu kada kuri’a cewa za su iya yin hakan. Ta bayyana cewa dole ne ‘yan siyasa masu son shugabanci su fito su yi Allah wadai da wannan barazanar.

Ta ce don kauce wa shakku, barazanar da kungiyar da ke yankin kudu maso gabas ke yi na tsorata masu zabe, inda ta jaddada cewa wadanda ke bayansu su sani cewa za a yi musu tirjiya.

Kungiyar ta yi nuni da cewa so da yawa tana nanata matsayarta da kuma sauran kungiyoyin da ke kishin kasa masu muradin ganin an gudanar da zaben 2023 a duk fadin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariIPOBNEFZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Kamfanin Samar Da Wutar Lantarki Mai Aiki Da Hasken Rana Na Zambiya Ya Fara Aiki

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

Related

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

7 days ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

7 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

4 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

4 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 month ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

Sojoji Sun Kashe 'Yan Bindiga 7, Sun Kwato Makamai A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

August 22, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

August 22, 2025
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

August 22, 2025
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

August 22, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.