ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Arewa

Ƙungiyar Matasan Arewa Mazauna Legas, ta jaddada kira ga al’ummar arewa da cewa bai kamata yankin ya yi sakaci har ya koma gidan jiya ba dangane da halin ha’ula’in da aka jefa shi ciki na tashe-tashen hankula da ƙangin talauci da karayar tattalin arziki.

Ƙungiyar ta sake nanata kiran ne sakamakon abin da ta kira “yunƙurin wasu marasa kishin al’ummar yankin na sake mayar da shi gidan jiya domin biyan muradun ƙashin kansu a zaɓen 2023 da ke tafe”.

  • 2023: Buhari So Ya Ke APC Ta Fadi Zabe – Ganduje
  • Shirin Kawo Karshen Yi Wa Mata Kaciya Nan Da 2030

Ƙungiyar wadda ta yi kiran ta bakin shugabanta, Alhaji Ibrahim Yaro Galadanci, ta ƙara da cewa dangane da zaɓen 2023 musammam na shugaban ƙasa mun ji yadda wasu shugabanni daga arewa suke ɓaɓatu domin cikar burinsu na son zuciya, suna so a goyi bayan waɗanda za su ƙara kashe mana yanki, marasa riƙon amana, to muna faɗa wa mutanen arewa cewa wannan baa bin amicewa ba ne a gare su, sannan su kuma masu yi su san cewa komai nisan jifa ƙasa zai sauko.”

ADVERTISEMENT

Ƙungiyar ta ci gaba da cewa tun daga dawowar mulkin dimokuraɗiyya ake wa yankin zagon ƙasa kuma idan har ba a farga a wannan lokaci na zaɓe ba, za a yi aikin da-na-sani.

“Domin lokaci ya yi da za mu zama tsintsiya maɗaurinmu ɗaya, wallahi tsakanin musulmin arewa da kiristocin arewa kowa ya sani tun a shekarar 1999 aka shirya kawar da dukkan ‘yan arewa daga doran ƙasa, aka dinga yi mana kisan gilla, ana ƙona dukiyarmu amma sabo da baragurbin shugabanni da suka mayar da mu saniyar ware, babu wasu masu ƙwatar wa ‘yan arewa ‘yanci. Duk inda ake rigima ɗan arewa ake kashewa, waye bai da masaniyar hakan a wannan lokacin.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Dan haka muna kira da babbar murya, babu yaudara wallahi, lallai mu ƙwatar wa kanmu ‘yanci domin mafitarmu a yanzu shi ne haɗin kai mai ƙarfin gaske wanda dole mu samu sauyi da taimakon Allah, mu yi ƙoƙarin haɗa kan kwankwaso da Al-Musatapa domin arewa muna da makama. Duk arzikin da Allah ya shinfiɗa a ƙarƙashin ƙasa yana yankin arewa, tun daga kan Gold (Zinare) da manyan ma’adanai waɗanda ka da mu yi sake masu cewa su ne shugabaninmu su sayar da mu tun da sun kasance karnukan farautar waɗansu.” In ji shugaban ƙungiyar.

Har ila yau, ƙungiyar ta yi waiwaye adon tafiya game da manyan rikice-rikicen da ta ce an ƙirƙiro domin wargaza yankin, “masu haɗa waɗannan rigingimu da makirce-makice sun cire rahamar Allah a zukatansu, suka bari aka ƙirƙiro Boko Haram, aka ƙirƙiro rigimar manoma da makiyaya, saboda dukiyar da take Maiduguri da Yobe da Zamfara da Sakkoto da Neja da Kogi duk duniya babu ƙasar da za ta iya ja da arzikin da Allah ya yi mana, amma kuma ga mutanenmu suna cikin yunwa da talauci, don haka mu zaɓi ‘yan siyasa masu kishin al’umma da za su iya kawo gyara.”

Alhaji Ibrahim ya kuma nunar da cewa ba saboda wata jam’iyya ɗaya suke waɗannan kiraye-kirayen ba, yana mai cewa, “dan ba ma jam’iyya, abin da muke so mutanenmu na arewa su yi kawai, mu yi ƙoƙarin janyo hankulan `yan’uwanmu waɗanda suna cikin duhu da su dawo hanya domin mu ceci rayuwarmu, muna da arziki, don haka a daina yi mana kisan gillah. Sannan a yi ƙoƙarin daidaita tafiyar Majo Hamza Al-Musatapa da Kwankwaso, wallahi alheri ne a gare mu, dan Allah mu yi wa azzaliman tsofaffin shugabaninmu bara’a lokaci domin wannan ne lokaci mafi dacewa da za mu nema wa kanmu mafita.”

Wakazalika, ƙungiyar ta matasan arewa ta ce taron da gwamnonin Nijeriya suka yi da shugaban ƙasa a kan batun canjin kuɗi ba don talakawa suka yi ba, “taron da suka je Abuja suka samu shugaban ƙasa a fadarsa sabo da maganar canjing kuɗi domin kansu ne ba don talaka ba. Don su ma za su yi asara shi ya sa suka je, saboda mutum nawa aka sace a arewa ban da waɗanda aka yi wa kisan gilla, me ya sa babu wanda ya ce ya kamata su yi ƙungiya dan hakan? Lallai ya zama wajibi mutane mu farka mu yi wa kanmu ƙiyamullaili.” In ji Galadanci.

Arewa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

Kalubalen Da Ka Iya Barazana Ga Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.