ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Arewa An Sha Mu Mun Warke, Bai Kamata Mu Koma Gidan Jiya Ba – Matasan Arewa A Kudu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Arewa

Ƙungiyar Matasan Arewa Mazauna Legas, ta jaddada kira ga al’ummar arewa da cewa bai kamata yankin ya yi sakaci har ya koma gidan jiya ba dangane da halin ha’ula’in da aka jefa shi ciki na tashe-tashen hankula da ƙangin talauci da karayar tattalin arziki.

Ƙungiyar ta sake nanata kiran ne sakamakon abin da ta kira “yunƙurin wasu marasa kishin al’ummar yankin na sake mayar da shi gidan jiya domin biyan muradun ƙashin kansu a zaɓen 2023 da ke tafe”.

  • 2023: Buhari So Ya Ke APC Ta Fadi Zabe – Ganduje
  • Shirin Kawo Karshen Yi Wa Mata Kaciya Nan Da 2030

Ƙungiyar wadda ta yi kiran ta bakin shugabanta, Alhaji Ibrahim Yaro Galadanci, ta ƙara da cewa dangane da zaɓen 2023 musammam na shugaban ƙasa mun ji yadda wasu shugabanni daga arewa suke ɓaɓatu domin cikar burinsu na son zuciya, suna so a goyi bayan waɗanda za su ƙara kashe mana yanki, marasa riƙon amana, to muna faɗa wa mutanen arewa cewa wannan baa bin amicewa ba ne a gare su, sannan su kuma masu yi su san cewa komai nisan jifa ƙasa zai sauko.”

ADVERTISEMENT

Ƙungiyar ta ci gaba da cewa tun daga dawowar mulkin dimokuraɗiyya ake wa yankin zagon ƙasa kuma idan har ba a farga a wannan lokaci na zaɓe ba, za a yi aikin da-na-sani.

“Domin lokaci ya yi da za mu zama tsintsiya maɗaurinmu ɗaya, wallahi tsakanin musulmin arewa da kiristocin arewa kowa ya sani tun a shekarar 1999 aka shirya kawar da dukkan ‘yan arewa daga doran ƙasa, aka dinga yi mana kisan gilla, ana ƙona dukiyarmu amma sabo da baragurbin shugabanni da suka mayar da mu saniyar ware, babu wasu masu ƙwatar wa ‘yan arewa ‘yanci. Duk inda ake rigima ɗan arewa ake kashewa, waye bai da masaniyar hakan a wannan lokacin.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

“Dan haka muna kira da babbar murya, babu yaudara wallahi, lallai mu ƙwatar wa kanmu ‘yanci domin mafitarmu a yanzu shi ne haɗin kai mai ƙarfin gaske wanda dole mu samu sauyi da taimakon Allah, mu yi ƙoƙarin haɗa kan kwankwaso da Al-Musatapa domin arewa muna da makama. Duk arzikin da Allah ya shinfiɗa a ƙarƙashin ƙasa yana yankin arewa, tun daga kan Gold (Zinare) da manyan ma’adanai waɗanda ka da mu yi sake masu cewa su ne shugabaninmu su sayar da mu tun da sun kasance karnukan farautar waɗansu.” In ji shugaban ƙungiyar.

Har ila yau, ƙungiyar ta yi waiwaye adon tafiya game da manyan rikice-rikicen da ta ce an ƙirƙiro domin wargaza yankin, “masu haɗa waɗannan rigingimu da makirce-makice sun cire rahamar Allah a zukatansu, suka bari aka ƙirƙiro Boko Haram, aka ƙirƙiro rigimar manoma da makiyaya, saboda dukiyar da take Maiduguri da Yobe da Zamfara da Sakkoto da Neja da Kogi duk duniya babu ƙasar da za ta iya ja da arzikin da Allah ya yi mana, amma kuma ga mutanenmu suna cikin yunwa da talauci, don haka mu zaɓi ‘yan siyasa masu kishin al’umma da za su iya kawo gyara.”

Alhaji Ibrahim ya kuma nunar da cewa ba saboda wata jam’iyya ɗaya suke waɗannan kiraye-kirayen ba, yana mai cewa, “dan ba ma jam’iyya, abin da muke so mutanenmu na arewa su yi kawai, mu yi ƙoƙarin janyo hankulan `yan’uwanmu waɗanda suna cikin duhu da su dawo hanya domin mu ceci rayuwarmu, muna da arziki, don haka a daina yi mana kisan gillah. Sannan a yi ƙoƙarin daidaita tafiyar Majo Hamza Al-Musatapa da Kwankwaso, wallahi alheri ne a gare mu, dan Allah mu yi wa azzaliman tsofaffin shugabaninmu bara’a lokaci domin wannan ne lokaci mafi dacewa da za mu nema wa kanmu mafita.”

Wakazalika, ƙungiyar ta matasan arewa ta ce taron da gwamnonin Nijeriya suka yi da shugaban ƙasa a kan batun canjin kuɗi ba don talakawa suka yi ba, “taron da suka je Abuja suka samu shugaban ƙasa a fadarsa sabo da maganar canjing kuɗi domin kansu ne ba don talaka ba. Don su ma za su yi asara shi ya sa suka je, saboda mutum nawa aka sace a arewa ban da waɗanda aka yi wa kisan gilla, me ya sa babu wanda ya ce ya kamata su yi ƙungiya dan hakan? Lallai ya zama wajibi mutane mu farka mu yi wa kanmu ƙiyamullaili.” In ji Galadanci.

Arewa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Next Post
Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

Kalubalen Da Ka Iya Barazana Ga Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.