• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makamai Ba Za Su Tabbatar Da Zaman Lafiya Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Makamai Ba Za Su Tabbatar Da Zaman Lafiya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekara guda ke nan da aukuwar rikici tsakanin Ukraine da Rasha, rikicin da kawo yanzu ya haddasa miliyoyin ‘yan gudun hijira, baya ga kuma mummunan tasirin da ya haifar ta fannonin samar da abinci da makamashi da ma farfadowar tattalin arzikin duniya.

Da Rasha da Ukraine da ma sauran kasashen Turai da ke kusa da fagen yakin, har ma da sauran kasashen duniya da suka hada da na Afirka, duk sun dandana kudar rikicin, akasin yadda Amurka ke cin moriyar siyasa da mummunar riba ta hanyar samar da makamai.

  • Zaben 2023: ‘Yan Daba Sun Sace Na’urar BVAS 8 A Delta Da Katsina

Alkaluman da majalisar gudanarwar kasar Amurka ta samar sun nuna cewa, a shekarar kudi ta 2022, yawan makaman da kasar Amurka ta sayar zuwa ketare ya karu da kimanin 50% bisa na shekarar 2021, kuma daya daga cikin dalilan haka shi ne barkewar rikici a tsakanin Ukraine da Rasha.

Kwanan baya, shugaban kasar Amurka Joe Biden ya kai ziyara ta ba zata Ukraine, inda ya sanar da karin gudummawar soja da za su kai dala miliyan 500 da za ta samar wa Ukraine, kuma hakan na zuwa ne kasa da wata guda, bayan wata gudummawar soja da ta sanar a farkon wannan wata. Labarin da kamfanin dillancin labarai na AP ya bayar ya shaida cewa, gaba dayan gudummawar soja da Amurka ta samar wa Ukraine ya zarce dala biliyan 50.

A shekarar da ta gabata ce rikici ya barke tsakanin Ukraine da Rasha, sakamakon yadda Amurka ta rura wutar rikicin, yanzu haka, shugaban Amurka ya kara rura wutar a ziyararsa, a maimakon ya taimaka ga tabbatar da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

A yayin da ake cika shekara guda da aukuwar rikicin, ma’aikatar harkokin waje ta kasar Sin ta bayar da wata takarda a jiya, inda daga wasu fannoni 12 ta nanata matsayinta na daidaita matsalar Ukraine a siyasance, a cewarta, yin shawarwari shi ne hanya daya tilo wajen daidaita rikicin.

Idan mun waiwayi baya, za mu ga cewa, kasar Sin ta sha neman tabbatar da sulhu a tsakanin kasashen biyu. Ko da a kwanakin baya ma, ta yi shawarwari a kai tsaye da Ukraine da ma Rasha bi da bi, inda take kokarin neman sassauta mummunan yanayin da ake ciki.

A cikin shekarar da ta gabata, kasar Sin ba ta taba tsayawa tana kallon rikicin ba, ballantana ta rura wutar rikicin, kuma hakan ya faru ne sakamakon irin ra’ayoyi na “zama lafiya da juna da martaba bambance-bambance” da “zama lafiya da kasa da kasa” da “kawar da yake-yake a duniya” da ke cikin al’adun gargajiya na tsawon tarihi na shekaru sama da 5000 na kasar Sin, ra’ayoyin da a zamanin yau aka bayyana su a cikin shawarar kiyaye tsaron duniya da kasar ta gabatar, wato a rika yin shawarwari a maimakon yin fito na fito, kuma a yi hadin gwiwa a maimakon kulla kawance, da ma cin moriyar juna a maimakon cin nasara daga faduwar wani bangare.

Matsalar Ukraine ta kara nunawa al’umma cewa, tsaro ba hakkin musamman na wasu kasashe ba ne, kuma bai kamata a lalata tsaron wata kasa don tabbatar da na wata ba, kuma habaka kawancen soja ba zai haifar da kome ba, illa ya lalata tsaron shiyya.

Makomar dan Adam daya ce. Tabbatar da dauwamammen ci gaban duniya, ta yadda al’ummar kowace kasa za ta iya rayuwa cikin kwanciyar hankali da walwala, burinmu ne na bai daya. Duk wahalar da za a fuskanta, ya zama dole a daidaita matsalar Ukraine a siyasance. Aikin da muka sanya a gaba shi ne a tabbatar da tsagaita bude wuta a tsakanin kasashen biyu cikin gaggawa, kuma makamai ba za su tabbatar da zaman lafiya ba. (Mai zane:Mustapha Bulama)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 5 Sun Jikkata Yayin Da Boko Haram Suka Kai Hari Wajen Zabe A Borno

Next Post

Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

4 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

4 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

5 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

7 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

8 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

10 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

Da Dumi-Dumi: Obi Ya Lashe Mazabar Shugaban Jam'iyyar APC Na Kasa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.