• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: PDP Ta Gargadi Tinubu Kan Ikirarin Nasara Bayan Gwamnonin Arewa Sun Gaza Ceto Shi

by Muhammad
2 years ago
in Siyasa
0
Zaben 2023: PDP Ta Gargadi Tinubu Kan Ikirarin Nasara Bayan Gwamnonin Arewa Sun Gaza Ceto Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa a jam’iyyar PDP, ta gargadi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, da kada ya ba kansa nasara a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya na shekarar 2023, yana mai cewa gwamnonin Arewa da yake sa ran za su ba ba shi kuri’u sun gaza sosai.

Kwamitin ya kuma bukaci shugaban kasa, Muhammadu Buhari, da ya ja kunnen Tinubu kan yin ikirarin nasara a zaben na 2023.

  • INEC Ta Dage Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisun Tarayya Zuwa Yau Lahadi A Yenagoa
  • Atiku Ya Lashe Rumfar Zaben Mataimakin Peter Obi, Datti Baba-Ahmed

Kwamitin kamfen din ya bayyana hakan lokacin da yake mayar da martani ga wata kafar yada labarai da ta buga wanda PDP ta ce mallakin Tinubu ne.

Kafofin yada labaran sun yi ikirarin cewa Tinubu ne ke kan gaba a shiyyar Arewa maso Yamma da Kudu maso Yamma da kuma Arewa ta Tsakiya na kasa.

Sai dai Daraktan Sadarwar da Dabaru na
Kwamitin yakin neman zaben Atiku/Okowa, Cif Dele Momodu, wanda ya sanya hannu a wata sanarwa a ranar Lahadi, ya ce Tinubu ne kadai dan takara daya tilo da jam’iyyun adawa suka lalata yankinsa na Kudu maso Yamma a jihohin Legas, Ogun, Ondo, Oyo, Osun da Ekiti.

Labarai Masu Nasaba

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

Ya ce, “Dazun nan hankalinmu ya karkata ga labarin da jaridar ta buga mai hatsarin gaske da ke bayar da nasara ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu. Jaridar da aka ce mallakin Tinubu ce.

“A jiya ne muka ga yadda ’yan barandar APC da mutanensu suka mamaye titunan Legas suna kona akwatunan zabe da takardu da kuma nuna rashin da’a.

Duk da yunƙuri na satar nasara, APC ta yi asarar mafi muni a mafi yawan wuraren zaɓe a Legas. Haka ya faru a Kano.

A safiyar yau mun wayi gari mun karanta labarin karya da karyar da jaridar Tinubu suka buga.

“Tinubu ya dan takara ne daya tilo da jam’iyyun adawa suka lalata masa Kudu maso Yamma a Legas, Ogun, Ondo, Oyo, Osun da Ekiti. Yawancin Gwamnonin Arewa da ya sa ran za su taimaka masa wajen samun kuri’u a yankunan Arewa sun kasa kai wa ga kuri’un da ake bukata. Ya gaza a Kudu maso Gabas da Kudu Kudu.

“Dan takara daya tilo a kasa shi ne dan takarar shugaban kasa na PDP, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, a matsayinsa na dan kasa mai kishin kasa, ba zai taba yin gaggawar shiga kafafen yada labarai don neman nasara.” cewarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AtikuPDPTunibuZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben 2023: INEC Za Ta Fara Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa

Next Post

Zaben 2023: INEC Ta Dage Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Zuwa Karfe 6 Na Yamma

Related

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

1 day ago
Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

3 days ago
Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
Siyasa

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

6 days ago
Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani
Siyasa

Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani

7 days ago
Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba
Labarai

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

1 week ago
Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka
Siyasa

Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka

1 week ago
Next Post
Zaben 2023: INEC Za Ta Fara Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa

Zaben 2023: INEC Ta Dage Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Zuwa Karfe 6 Na Yamma

LABARAI MASU NASABA

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

May 11, 2025
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

May 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.