ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: PDP Ta Gargadi Tinubu Kan Ikirarin Nasara Bayan Gwamnonin Arewa Sun Gaza Ceto Shi

by Muhammad
3 years ago
PDP

Kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa a jam’iyyar PDP, ta gargadi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, da kada ya ba kansa nasara a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya na shekarar 2023, yana mai cewa gwamnonin Arewa da yake sa ran za su ba ba shi kuri’u sun gaza sosai.

Kwamitin ya kuma bukaci shugaban kasa, Muhammadu Buhari, da ya ja kunnen Tinubu kan yin ikirarin nasara a zaben na 2023.

  • INEC Ta Dage Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisun Tarayya Zuwa Yau Lahadi A Yenagoa
  • Atiku Ya Lashe Rumfar Zaben Mataimakin Peter Obi, Datti Baba-Ahmed

Kwamitin kamfen din ya bayyana hakan lokacin da yake mayar da martani ga wata kafar yada labarai da ta buga wanda PDP ta ce mallakin Tinubu ne.

ADVERTISEMENT

Kafofin yada labaran sun yi ikirarin cewa Tinubu ne ke kan gaba a shiyyar Arewa maso Yamma da Kudu maso Yamma da kuma Arewa ta Tsakiya na kasa.

Sai dai Daraktan Sadarwar da Dabaru na
Kwamitin yakin neman zaben Atiku/Okowa, Cif Dele Momodu, wanda ya sanya hannu a wata sanarwa a ranar Lahadi, ya ce Tinubu ne kadai dan takara daya tilo da jam’iyyun adawa suka lalata yankinsa na Kudu maso Yamma a jihohin Legas, Ogun, Ondo, Oyo, Osun da Ekiti.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

Ya ce, “Dazun nan hankalinmu ya karkata ga labarin da jaridar ta buga mai hatsarin gaske da ke bayar da nasara ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu. Jaridar da aka ce mallakin Tinubu ce.

“A jiya ne muka ga yadda ’yan barandar APC da mutanensu suka mamaye titunan Legas suna kona akwatunan zabe da takardu da kuma nuna rashin da’a.

Duk da yunƙuri na satar nasara, APC ta yi asarar mafi muni a mafi yawan wuraren zaɓe a Legas. Haka ya faru a Kano.

A safiyar yau mun wayi gari mun karanta labarin karya da karyar da jaridar Tinubu suka buga.

“Tinubu ya dan takara ne daya tilo da jam’iyyun adawa suka lalata masa Kudu maso Yamma a Legas, Ogun, Ondo, Oyo, Osun da Ekiti. Yawancin Gwamnonin Arewa da ya sa ran za su taimaka masa wajen samun kuri’u a yankunan Arewa sun kasa kai wa ga kuri’un da ake bukata. Ya gaza a Kudu maso Gabas da Kudu Kudu.

“Dan takara daya tilo a kasa shi ne dan takarar shugaban kasa na PDP, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, a matsayinsa na dan kasa mai kishin kasa, ba zai taba yin gaggawar shiga kafafen yada labarai don neman nasara.” cewarsa.

PDP
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Atiku
Siyasa

Atiku Ya Naɗa Kenneth Okonkwo A Matsayin Kakakin Yaƙin Neman Zaɓensa

July 2, 2026
‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi
Manyan Labarai

‘Yan Adawa Sun Mayar Da Matsalar Tsaro Siyasa – Yusuf Gagdi

July 1, 2026
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Siyasa

Tinubu Ya Shimfiɗa Wa Arewacin Nijeriya Ayyuka Sama Da Kowane Shugaban Ƙasa – Uba Sani

July 1, 2026
Next Post
Zaben 2023: INEC Za Ta Fara Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa

Zaben 2023: INEC Ta Dage Bayyana Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Zuwa Karfe 6 Na Yamma

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.