• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tuni farashin kayayyakin amfanin gona ya yi tashin gwauron zabi a sassan duniya daban daban, sakamakon rikicin Rasha da Ukraine, wanda a yanzu ya zarce watanni uku da barkewa.

Alkaluman shirin samar da abinci na MDD sun tabbatar da cewa, duniya ba ta taba ganin kalubalen tsadar cimaka sama da na wannan lokaci ba, tun bayan yakin duniya na biyu, lamarin da kuma ke zuwa a gabar da duniya ke fuskantar tasirin annobar COVID-19, wadda ita ma ta haifar da komadar tattalin arzikin duniya.

  • Jawabin Xi Jinping Ya Kara Azama Kan Aiwatar Da Shawarar Bunkasa Duniya

Yayin da kasashen yammacin duniya ke ta kokarin dora alhakin hauhawar farashin kayayyakin amfanin gona ga kasar Rasha, su ma a nasu bangare sun taka rawar gani wajen ingiza girman wannan matsala.

Ga misali, shi kan shi rikicin Rasha da Ukraine, kasashe biyu masu fitar da tarin albarkatun gona ga sassa daban daban na duniya, ya samo asali ne sakamakon kokarin fadada ikon kungiyar tsaro ta NATO zuwa gabashin turai. Kuma duk da yunkuri da aka yi na hawa teburin shawara tsakanin Rasha da Ukraine, Amurka a nata bangare, ta yi ta kokarin rura wutar rikicin ta hanyar samarwa Ukraine makamai domin tunkarar Rasha, wanda hakan ke kara tsawaita mummunan tasirin tashin hankalin.

A zahiri, tsawaitar wannan tashin hankali zai ci gaba da ingiza asarar da Rasha da Ukraine za su kirga, a hannu guda kuma, hakan zai haifar da kamfar abinci a sassa masu yawa na duniya, musamman kasashe masu tasowa, dake dogaro sosai kan cimakar da ake fitarwa daga kasashen biyu.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Ko shakka ba bu, yunkurin Amurka na kakaba takunkumin cinikayyar albarkatun gona da takin zamani da kasar Rasha ke fitarwa, ya haifar da hauhawar farashin cimaka da kaso sama da 30 bisa dari a kasashe masu tasowa.

Irin wadannan kasashe masu tasowa, da sauran masu raunin tattalin arziki, na shan matsin lambar rayuwa, sakamakon manufofin takara, da kokarin tabbatar da iko na wasu kasashen yamma, wannan yanayi ne da bai dace ba, domin kuwa, kamata yayi manyan kasashen yamma masu karfin fada a ji, su taimaka wajen fitar da kasashe masu tasowa daga wahalhalu, maimakon aiwatar da matakai na kara jefa su cikin mawuyacin hali. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Batun Mika ‘Yan Gudun Hijira Ya Nuna Halayyar Kasashen Yamma

Next Post

Yadda Wata Budurwa Ta Yi Garkuwa Da Kanta

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

16 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

17 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

19 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

20 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

21 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

22 hours ago
Next Post
Yadda Wata Budurwa Ta Yi Garkuwa Da Kanta

Yadda Wata Budurwa Ta Yi Garkuwa Da Kanta

LABARAI MASU NASABA

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

July 12, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

July 12, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

July 12, 2025
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.