• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Gwamnoni Masu Barin Gado Da Suka Fadi Zaben Kujerar Sanata 

by Abubakar Abba
3 years ago
Zaben 2023

Akalla gwamnoni shida masu barin gado ne a fadin kasar nan suka gaza kai bantensu bayan tsayawa takarar kujerar Sanata a mazabunsu.

Gwanonin wadanda suka yi wa’adin shekara takwas a kan kujerunsu, sun sha kasa ne a zabukan Sanatan da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabirairu 2023.

  • Da Dumi-Dumi: PDP, LP Da ADC Dun Bukaci INEC Ta Gudanar Da Sabon Zabe
  • Peter Obi Ya Lashe Birnin Tarayya

Tun bayan dawowar mulkin dimokuradiyya a 1999, an danganta majalisar wakilai da kuma ta dattijai a matsayin wata mafakar tsofaffin gwamnoni.

Kimanin tsofaffin gwamnoni 20 aka zaba zuwa ga majalisa ta tara a 2019.

Tsofaffin gwanonin da a yanzu ke majalisar dattawa su ne, Rochas Okorocha daga Jihar Imo, Ibikunle Amosun daga Jihar Ogun, Abdulaziz Yari daga Jihar Zamfara Kabiru Gaya daga Jihar Kano, Abdullahi Adamu daga Jihar Nasarawa, Chimaroke Nnamani daga Jihar Enugu, Kalu daga Jihar Abia, Gabriel Suswam daga Jihar Binuwe da kuma Ibrahim Shekarau daga Jihar Kano da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Wadanda a bana suka shiga zaben sun hada da, gwamnan Jihar Ebonyi David Umahi, gwamnan Jihar Neja Abubakar Bello da kuma gwamnan Abia Okezie Ikpeazu wadanda suka lashe zaben na ranar asabar.

Sai dai, Atiku Bagudu na Jihar Kebbi ya fadi yayin da ba a bayyana na gwaman Sakkwato Aminu Tambuwal ba.

Tsofaffin gwanonin da suka lashe zaben Sanata su ne, Adams Oshiomhole daga Jihar Edo sai kuma tsohon gwamnan Akwa Ibom Godswill Akpabio.

Ga jerin sunayen gwamonin masu barin gado da suka gaza lashe zaben bayan sun kammala wa’adin mulkinsu a watan Mayu 29, 2023.

Dan takarar Sanata na APC Titus Zam ya kayar da Samuel Ortom gwaman Jihar Binuwe a zaben Sanata na mazabar Binuwe ta Arewa Maso Gabas, inda Zam ya samu kuri’u 143,151, Ortum gwannan PDP na G-5, ya samu kuri’u 106,882, sai LP ta samu kuri’u 51,950.

Gwamna Ifeanyi Ugwuanyi ya gaza lashe zaben Sanata na mazabar Enugu ta Gabas.

Dan takarar Sanata a LP Okechukwu Ezea ne INEC ta sanar ya lashe zaben, inda ya samu kuri’u 104,948, Ugwuanyi kuma ya samu kuri’u 46,948.

Akwai kuma gwamnan Jihar Taraba Darius Ishaku wanda ya sha kasa a zaben mazabar Taraba ta Kudu, inda dan takara David Jimkuta, daga APC ya kayar da shi bayan ya samu kuri’u 85,415 Ishaku kuma ya samu kuri’u 45,708.

Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong kuma darakta-janar na kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, dan takarar Sanata a PDP Bali Ninkap Napoleon ya kayar da shi bayan ya samu kuri’u 148,844 inda Lalong ya samu kuri’u 91,674.

Gwannan Jihar Koros Ribas Ben Ayade ya sha kasa a hannun Jarigbe Agom-Jarigbe dan takarar Sanata a jam’iyyar PDP, wanda dama can shi ne yake a kan kujerar, inda Agom ya samu kuri’u 76,145 sai kuma Ayade ya samu kuri’u 56,595.

Ayade kafin a zabe shi gwamna, ya kasance zababben Sanata ne daga

2011 zuwa 2015, inda a zaben 2023, ya so ya sake komawa majalisar dattawa

don ya wakilci mazabar Koros Ribas ta Arewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Next Post
Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.