• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Gwamnoni Masu Barin Gado Da Suka Fadi Zaben Kujerar Sanata 

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben 2023: Gwamnoni Masu Barin Gado Da Suka Fadi Zaben Kujerar Sanata 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla gwamnoni shida masu barin gado ne a fadin kasar nan suka gaza kai bantensu bayan tsayawa takarar kujerar Sanata a mazabunsu.

Gwanonin wadanda suka yi wa’adin shekara takwas a kan kujerunsu, sun sha kasa ne a zabukan Sanatan da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabirairu 2023.

  • Da Dumi-Dumi: PDP, LP Da ADC Dun Bukaci INEC Ta Gudanar Da Sabon Zabe
  • Peter Obi Ya Lashe Birnin Tarayya

Tun bayan dawowar mulkin dimokuradiyya a 1999, an danganta majalisar wakilai da kuma ta dattijai a matsayin wata mafakar tsofaffin gwamnoni.

Kimanin tsofaffin gwamnoni 20 aka zaba zuwa ga majalisa ta tara a 2019.

Tsofaffin gwanonin da a yanzu ke majalisar dattawa su ne, Rochas Okorocha daga Jihar Imo, Ibikunle Amosun daga Jihar Ogun, Abdulaziz Yari daga Jihar Zamfara Kabiru Gaya daga Jihar Kano, Abdullahi Adamu daga Jihar Nasarawa, Chimaroke Nnamani daga Jihar Enugu, Kalu daga Jihar Abia, Gabriel Suswam daga Jihar Binuwe da kuma Ibrahim Shekarau daga Jihar Kano da sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Wadanda a bana suka shiga zaben sun hada da, gwamnan Jihar Ebonyi David Umahi, gwamnan Jihar Neja Abubakar Bello da kuma gwamnan Abia Okezie Ikpeazu wadanda suka lashe zaben na ranar asabar.

Sai dai, Atiku Bagudu na Jihar Kebbi ya fadi yayin da ba a bayyana na gwaman Sakkwato Aminu Tambuwal ba.

Tsofaffin gwanonin da suka lashe zaben Sanata su ne, Adams Oshiomhole daga Jihar Edo sai kuma tsohon gwamnan Akwa Ibom Godswill Akpabio.

Ga jerin sunayen gwamonin masu barin gado da suka gaza lashe zaben bayan sun kammala wa’adin mulkinsu a watan Mayu 29, 2023.

Dan takarar Sanata na APC Titus Zam ya kayar da Samuel Ortom gwaman Jihar Binuwe a zaben Sanata na mazabar Binuwe ta Arewa Maso Gabas, inda Zam ya samu kuri’u 143,151, Ortum gwannan PDP na G-5, ya samu kuri’u 106,882, sai LP ta samu kuri’u 51,950.

Gwamna Ifeanyi Ugwuanyi ya gaza lashe zaben Sanata na mazabar Enugu ta Gabas.

Dan takarar Sanata a LP Okechukwu Ezea ne INEC ta sanar ya lashe zaben, inda ya samu kuri’u 104,948, Ugwuanyi kuma ya samu kuri’u 46,948.

Akwai kuma gwamnan Jihar Taraba Darius Ishaku wanda ya sha kasa a zaben mazabar Taraba ta Kudu, inda dan takara David Jimkuta, daga APC ya kayar da shi bayan ya samu kuri’u 85,415 Ishaku kuma ya samu kuri’u 45,708.

Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong kuma darakta-janar na kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, dan takarar Sanata a PDP Bali Ninkap Napoleon ya kayar da shi bayan ya samu kuri’u 148,844 inda Lalong ya samu kuri’u 91,674.

Gwannan Jihar Koros Ribas Ben Ayade ya sha kasa a hannun Jarigbe Agom-Jarigbe dan takarar Sanata a jam’iyyar PDP, wanda dama can shi ne yake a kan kujerar, inda Agom ya samu kuri’u 76,145 sai kuma Ayade ya samu kuri’u 56,595.

Ayade kafin a zabe shi gwamna, ya kasance zababben Sanata ne daga

2011 zuwa 2015, inda a zaben 2023, ya so ya sake komawa majalisar dattawa

don ya wakilci mazabar Koros Ribas ta Arewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnoni Masu Barin HadoTakarar SanataZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakiyar Wike Ta Lashe Zaben Sanatan Ribas Ta Yamma

Next Post

Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

Related

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

6 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

8 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

19 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

1 day ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

2 days ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 days ago
Next Post
Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.