ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Gwamnoni Masu Barin Gado Da Suka Fadi Zaben Kujerar Sanata 

by Abubakar Abba
3 years ago
Zaben 2023

Akalla gwamnoni shida masu barin gado ne a fadin kasar nan suka gaza kai bantensu bayan tsayawa takarar kujerar Sanata a mazabunsu.

Gwanonin wadanda suka yi wa’adin shekara takwas a kan kujerunsu, sun sha kasa ne a zabukan Sanatan da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabirairu 2023.

  • Da Dumi-Dumi: PDP, LP Da ADC Dun Bukaci INEC Ta Gudanar Da Sabon Zabe
  • Peter Obi Ya Lashe Birnin Tarayya

Tun bayan dawowar mulkin dimokuradiyya a 1999, an danganta majalisar wakilai da kuma ta dattijai a matsayin wata mafakar tsofaffin gwamnoni.

ADVERTISEMENT

Kimanin tsofaffin gwamnoni 20 aka zaba zuwa ga majalisa ta tara a 2019.

Tsofaffin gwanonin da a yanzu ke majalisar dattawa su ne, Rochas Okorocha daga Jihar Imo, Ibikunle Amosun daga Jihar Ogun, Abdulaziz Yari daga Jihar Zamfara Kabiru Gaya daga Jihar Kano, Abdullahi Adamu daga Jihar Nasarawa, Chimaroke Nnamani daga Jihar Enugu, Kalu daga Jihar Abia, Gabriel Suswam daga Jihar Binuwe da kuma Ibrahim Shekarau daga Jihar Kano da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Wadanda a bana suka shiga zaben sun hada da, gwamnan Jihar Ebonyi David Umahi, gwamnan Jihar Neja Abubakar Bello da kuma gwamnan Abia Okezie Ikpeazu wadanda suka lashe zaben na ranar asabar.

Sai dai, Atiku Bagudu na Jihar Kebbi ya fadi yayin da ba a bayyana na gwaman Sakkwato Aminu Tambuwal ba.

Tsofaffin gwanonin da suka lashe zaben Sanata su ne, Adams Oshiomhole daga Jihar Edo sai kuma tsohon gwamnan Akwa Ibom Godswill Akpabio.

Ga jerin sunayen gwamonin masu barin gado da suka gaza lashe zaben bayan sun kammala wa’adin mulkinsu a watan Mayu 29, 2023.

Dan takarar Sanata na APC Titus Zam ya kayar da Samuel Ortom gwaman Jihar Binuwe a zaben Sanata na mazabar Binuwe ta Arewa Maso Gabas, inda Zam ya samu kuri’u 143,151, Ortum gwannan PDP na G-5, ya samu kuri’u 106,882, sai LP ta samu kuri’u 51,950.

Gwamna Ifeanyi Ugwuanyi ya gaza lashe zaben Sanata na mazabar Enugu ta Gabas.

Dan takarar Sanata a LP Okechukwu Ezea ne INEC ta sanar ya lashe zaben, inda ya samu kuri’u 104,948, Ugwuanyi kuma ya samu kuri’u 46,948.

Akwai kuma gwamnan Jihar Taraba Darius Ishaku wanda ya sha kasa a zaben mazabar Taraba ta Kudu, inda dan takara David Jimkuta, daga APC ya kayar da shi bayan ya samu kuri’u 85,415 Ishaku kuma ya samu kuri’u 45,708.

Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong kuma darakta-janar na kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, dan takarar Sanata a PDP Bali Ninkap Napoleon ya kayar da shi bayan ya samu kuri’u 148,844 inda Lalong ya samu kuri’u 91,674.

Gwannan Jihar Koros Ribas Ben Ayade ya sha kasa a hannun Jarigbe Agom-Jarigbe dan takarar Sanata a jam’iyyar PDP, wanda dama can shi ne yake a kan kujerar, inda Agom ya samu kuri’u 76,145 sai kuma Ayade ya samu kuri’u 56,595.

Ayade kafin a zabe shi gwamna, ya kasance zababben Sanata ne daga

2011 zuwa 2015, inda a zaben 2023, ya so ya sake komawa majalisar dattawa

don ya wakilci mazabar Koros Ribas ta Arewa.

Zaben 2023
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

Sin Za Ta Ba Da Gudummawa Wajen Tafyar Da Harkokin Hakkin Dan Adam A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.