• English
  • Business News
Tuesday, September 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyare-gyare Sun Sa Zaman Al’umma Samun Ci Gaba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gyare-gyare Sun Sa Zaman Al’umma Samun Ci Gaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, ko kun jefa kuri’unku a babban zaben kasar Najeriya na wannan karo? Da fatan za a kammala ayyukan babban zaben lami lafiya, ta yadda za a aza harsashi na siyasa mai kyau ga ci gaban kasar Najeriya cikin shekaru masu zuwa.

A telabijin, na ga wani dan Najeriya da ya halarci babban zaben ya gaya ma manema labaru cewa, “Ya kamata mu jefa kuri’a, saboda muna bukatar wata sabuwar kasar Najeriya, da sauya abubuwa da yawa.” Maganarsa ta nuna ma’anar yin zabe, wato kawo sauye-sauye ga wata kasa, inda za a yi amfani da sabbin manufofi wajen daidaita matsalolin da ake fuskanta, da raya tattalin arziki, gami da kyautata zaman rayuwar jama’a.

Batun nan ya sa ni tunawa da wani taron da jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, mai mulki a kasar, ta gudanar da shi a birnin Beijing, a kwanakin nan, inda wani babban jigon da ake tattaunawa a kai shi ne yin gyare-gyare kan tsarin hukumomin kasar.

Abokaina da suka fahimci tsarin siyasa na kasar Sin, za su san cewa, kokarin yin kwaskwarima kan manufofi da tsarin hukumomi wata babbar manufa ce da kasar ke nacewa a kai. Cikin shekaru fiye da 70 bayan kafuwar Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, an yi babbar kwaskwarima kan tsare-tsaren hukumomin kasar har sau 13, inda aka takaita wasu hukumomi da ma’aikatansu, da inganta kwarewar hukumomin gwamnati ta fuskar samar da hidimomi ga al’umma, da sanya yanayin aikin mulki ya dace da tsarin baiwa kasuwa damar yin halinta, da dai makamantansu, tare da samun nagartaccen sakamako.

Idan mun dauki aikin takaita hukumomi a matsayin misali, wata kwaskwarimar da aka yi wa hukumomin kasar Sin a shekarar 2018 ita kadai, ta sa yawan ma’aikatun gwamnatin kasar ya ragu da wasu 8. Ta wannan hanya, an daidaita tsarin hukumomi, da samun karin jami’ai masu kwarewar aiki. Ban da haka, an rage ma jama’ar kasar nauyin biyan haraji, kana sun samu sauki sosai yayin da suke gudanar da wasu ayyuka a hukumomi daban daban.

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Wannan kwaskwarima ta nuna yadda gwamnatin kasar Sin ke iya sabunta tsare-tsare da kanta, inda take neman zamanintar da dabarun mulki a kai a kai, ba tare da tsoron gudanar da gyare-gyare kan hukumomin kasa kai tsaye ba, musammam da zummar tabbatar da ci gaban kasa da na zaman al’umma, da gamsar da daukacin al’ummun kasar. Ma iya cewa, dukkan nasarorin da kasar Sin ta samu a fannin raya tattalin arizki, cikin shekaru fiye da 40 da suka wuce, shaida ce ga yadda gyare-gyare ke haifar da ci gaban zaman al’umma.

To, tun da aikin kula da wata kasa na bukatar a yi masa kwaskwarima a kai a kai. Shin duniyarmu ita ma tana bukatar samun gyare-gyare a kan tsarinta?
Hayley Arceneaux, wata ‘yar saman jannati ce, wadda ta taba rubuta cewa, “ Yayin da nake hangen duniyar Earth daga sama, na ga a karkashin abubuwa masu kyan gani, akwai wasu abubuwa marasa kyau. Misali, ko da yake dukkanmu na rayuwa kan wannan duniya, amma mutanen da aka haife su a wannan bangare na duniya, da wadanda suke zama a waccan bangare, gibin zaman rayuwarsu ya yi yawa.”

A da can, wasu kasashen yammacin duniya masu karfi sun kafa wani tsarin duniya maras adalci, ta hanyar yake-yake, da mulkin mallaka, da raba ikon mallakar yankunan duniya tsakaninsu, wanda ke ci gaba da kasancewa a duniyarmu har zuwa yanzu. Sa’an nan wasu kasashe sun dade suna rike da ra’ayin “cin nasara daga faduwar wani bangare”, saboda haka suna ta neman toshe wa kasashe masu tasowa hanyar samun ci gaba.

Ganin wannan yanayin da ake ciki ne, ya sa kasar Sin ta dau niyyar kafa wata sabuwar huldar kasa da kasa, wadda ta daukaka ra’ayin hadin gwiwa da samun moriya tare, gami da gabatar da shawarar kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya.

Ayyukan kula da harkokin kasa da kasa ma suna bukatar a yi musu gyare-gyare, kana kasar Sin na ta kokarin samar da sauye-sauye da kwaskwarima kan tsare-tsaren duniya, ta yadda al’ummar dan Adam za ta dinga samun ci gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gogaggen Dan Jarida, Shehu Saulawa Ya Kwanta Dama

Next Post

2023: Kotu Ta Aike Da Mawallafin Jaridar WikkiTimes Gidan Yari Kan Zargin Haifar Da Fitina

Related

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

18 hours ago
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

18 hours ago
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci
Daga Birnin Sin

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

19 hours ago
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan
Daga Birnin Sin

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

20 hours ago
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

21 hours ago
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

23 hours ago
Next Post
2023: Kotu Ta Aike Da Mawallafin Jaridar WikkiTimes Gidan Yari Kan Zargin Haifar Da Fitina

2023: Kotu Ta Aike Da Mawallafin Jaridar WikkiTimes Gidan Yari Kan Zargin Haifar Da Fitina

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

September 2, 2025
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

September 2, 2025
NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

September 2, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

September 2, 2025
Zargin Cin Hanci: Babu Wani Shirin Tsige El-Rufai – Kakakin Majalisar Dokokin Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

September 2, 2025
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

2027: Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

September 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Daba 107 A Kano, Sun Ƙwato Makamai Da Ƙwayoyi

September 2, 2025
Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.