ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
GGI

“Kasa da kasa su kasance suna zaman daidaito da juna wajen sa hannun gudanar da harkokin duniya da ma yanke shawara da cin moriya” “Kada a tilasta kakaba dokokin cikin gida na wasu kasashe a kan sauran kasashe” “Nuna rashin amincewa da daukar matakai na kashin kai” “A yi kokarin daidaita gibin da ke tsakanin kasashe masu tasowa da kasashe masu ci gaba” “A dauki hakikanan matakai na hadin gwiwa”. A ranar 1 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jagoranci taron kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai (SCO) Plus a birnin Tianjin da ke arewacin kasar Sin, inda ya gabatar da Tsarin Shugabanci na Duniya wato “GGI” a takaice, shawarar da ta samar da mafita ga duniyar da ke fama da tashe-tashen hankula a halin yanzu.

A duniyar yau, aukuwar rikicin shiyya shiyya da matsalolin ci gaban tattalin arziki da rashin bin ka’idoji da dokoki da daukar matakai na kashin kai da kariyar ciniki da rashin tsarin shugabanci nagari a duniya, duk suna addabar kasashen duniya. Ta yaya za a inganta tsarin shugabanci na duniya, ya zama abin da ke bukatar a gano bakin zaren warware shi ga gamayyar kasa da kasa. To, faduwa ta zo daidai da zama bisa yadda kasar Sin ta gabatar da shawarar GGI.

“Ya kamata mu bi tsarin daidaito a kan ‘yancin yankunan kasa sau da kafa, ya kamata mu kiyaye bin dokokin kasa da kasa, ya kamata mu aiwatar da tsarin mu’amala da bangarori daban daban, ya kamata mu yi yekuwar amfani da tsarin da zai fi mayar da hankali a kan al’umma, kana ya kamata mu mai da hankali kan daukar matakai na hakika.” Ka’idoji biyar ke nan da ke cikin shawarar GGI, wadanda suka mai da hankali a kan ainihin matsalolin da ake fuskanta a tsarin shugabanci na duniya, tare da bayyana matsayi da dabarun da suka kamata a dauka domin gyara tsarin. Daga cikinsu “tsarin daidaito a kan ‘yancin yankunan kasa” ya zama tushen tsarin shugabanci na duniya. Kasa da kasa, manya da kanana, masu karfi ko marasa karfi, ya kamata su kasance daidai-wa-daida wajen sa hannu ga harkokin duniya. Ya zama dole a kawo karshen yadda wasu ‘yan tsirarrun kasashe kawai ke fada a ji a harkokin duniya, kuma ya kamata “a kara wakilcin kasashe masu tasowa da fito da muryoyinsu a duniya”, don kara inganta adalcin tsarin duniya. Sa’an nan, dokokin kasa da kasa su kasance masu tabbaci ga tsarin shugabanci na duniya, wadanda ya kamata kasa da kasa su rubuta su, da kiyaye su, da ma aiwatar da su. Har wa yau, yin mu’amala da bangarori daban daban ya zama hanyar da za a bi wajen gudanar da tsarin shugabancin duniya, kasancewar tsarin shugabancin duniya na shafar kowa da kowa, ya kamata a daidaita hadin gwiwa da juna a maimakon nuna fin karfi. Kazalika, ya kamata a mai da hankali a kan al’umma, a sabili da yadda kyautata rayuwar al’umma shi ne jigon ainihin burin da ake neman cimmawa wajen inganta tsarin shugabanci na duniya. Daga karshe, daukar hakikanan matakai ya kasance ginshiki na tsarin shugabancin duniya, don daidaita matsalolin da ke addabar kasa da kasa, musamman ma kasashe masu tasowa.

ADVERTISEMENT

Bana ake cika shekaru 80 da samun nasarar yaki da mulkin danniya a duniya da ma kafa majalisar dinkin duniya(MDD). A shekaru 80 da suka wuce, al’ummun duniya sun hada karfi da karfe wajen samun nasarar yaki da mulkin danniya, kuma kasancewar kasar Sin daga cikin muhimman kasashen da suka cimma nasarar yakin, ta hada kai da kasa da kasa wajen kafa MDD. A yau kuma, lokacin da tsarin shugabanci na duniya ke fuskantar sabbin matsaloli, kasar Sin a matsayinta na babbar kasa da ke kokarin sauke nauyin da ke bisa wuyanta, za ta tsaya tsayin daka wajen kiyaye tsarin duniya da ke karkashin ginshikin MDD, ta hada kai da kasashe masu neman ci gaba, don dada yin kokarin gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da ma tabbatar da zaman lafiya da ci gaba ga dukkanin bil Adama.

 

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

GGI
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fitar Da Shirin Shekaru 5 Ya Bude Sabo Babi Na Tsarin Ci Gaban Yankin HK
GGI
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu
  • Sulaiman
    Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana
  • Sulaiman
    Sana’ar Aike Da Sakwanni a Sin Ta Ci Gaba Da Bunkasa Cikin Kwanciyar Hankali

MASU ALAKA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka
Ra'ayi Riga

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

September 14, 2026
Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Next Post
NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

LABARAI MASU NASABA

Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu

Yadda Amurka Ta Mayar Wa Sin Da Kayan Tarihi Ya Nuna Kyakkyawan Fata Na Gina Dangantaka Mai Inganci A Tsakaninsu

September 18, 2026
Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai

Sin Ta Bukaci Japan Ta Fuskanci Tarihinta Na Mamayar Zalunci Tare Da Waiwaye Mai Zurfi A Kai

September 18, 2026
Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba

Atiku Ya Nemi Tinubu Ya Rage Farashin Man Fetur Don Sauƙaƙa Wa ’Yan Nijeriya Wahalar Da Suke Sha

September 18, 2026
Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana

Kasar Sin Ta Samu Jarin Waje Kimanin Yuan Biliyan 479.95 A Watanni 8 Na FarkonBana

September 18, 2026
Sana’ar Aike Da Sakwanni a Sin Ta Ci Gaba Da Bunkasa Cikin Kwanciyar Hankali

Sana’ar Aike Da Sakwanni a Sin Ta Ci Gaba Da Bunkasa Cikin Kwanciyar Hankali

September 18, 2026
‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

Neja: An Fesa Wani Abu A Ɗakin Da Aka Tsare Mu – Matashin Da Ya Tsira

September 18, 2026
Sin Da Amurka Na Ci Gaba Da Tuntubar Juna Game Da Shirye-shiryen Ganawar Shugabannin Kasashen Biyu Cikin Shekarar Nan

Sin Da Amurka Na Ci Gaba Da Tuntubar Juna Game Da Shirye-shiryen Ganawar Shugabannin Kasashen Biyu Cikin Shekarar Nan

September 18, 2026
Samun Ci Gaba Shi Ne Abu Mai Tushe Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam

Samun Ci Gaba Shi Ne Abu Mai Tushe Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam

September 18, 2026
Gwamnatin Najeriya Na Daukar Darasi Daga Salon Da Kasar Sin Ke Amfani Da Shi Na Kulla Alakar Diflomasiyya Ta Hanyar Jan Hankali Da Kyakkyawar Mu’amala

Gwamnatin Najeriya Na Daukar Darasi Daga Salon Da Kasar Sin Ke Amfani Da Shi Na Kulla Alakar Diflomasiyya Ta Hanyar Jan Hankali Da Kyakkyawar Mu’amala

September 18, 2026
ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

ASUU Ta Janye Yajin Aiki A Jami’ar Kaduna

September 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.