• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Harin Zamfara Da Kano

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Bola Ahmed Tinubu, zababben shugaban kasa ya bayyana cewa ‘yan fashi, ta’addanci da kashe-kashen hankali bai kamata su zama wurin zama a Nijeriya ba.

Ya bayyana ra’ayinsa ne kan hare-haren da ‘yan bindiga da mahara suka kai a karamar hukumar Maru a Jihar Zamfara a karshen mako da kuma garin Maigari da ke karamar hukumar Rimin Gado a Jihar Kano.

  • Ka Daina Gararamba A Titi Ka Tafi Kotu —Martanin APC Ga Atiku
  • Ba Za Mu Bari NNPP Ta Yi Magudin Zabe A Kano Ba —Gwamnatin Kano

Tinubu ya bayyana cewa an kashe jami’in ‘yan sanda da dan banga a harin da ‘yan bindiga suka kai a Zamfara.

“A harin na Kano, ‘yan bindiga sun kutsa gidan wani basarake inda suka harbe shi har lahira,” in ji zababben shugaban kasar.

Ya kara da cewa harin da aka kai garin Maru bayan an samu zaman lafiya a Zamfara, ya kara da cewa akwai bukatar a kara kaimi domin murkushe ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda gaba daya.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

“A matsayinmu na kasa dole ne mu hada kai domin mu fatattaki wadannan ‘yan ta’addanci gaba daya. Kashe-kashen rashin hankali da ta’asa irin wannan bai kamata su kasance a kasarmu ba,” in ji shi.

Ya jajantawa Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Mista Usman Baba, da gwamnatin Zamfara da iyalan jami’an tsaron da abin ya shafa game da rasuwar.

Tinubu ya kuma bukaci a gudanar da bincike kan kisan Hakimin Maigari a Jihar Kano, wanda shi ne mahaifin Shugaban karamar Hukumar Rimin Gado, Mista Munir Maigari.

Ya mika ta’aziyyarsa ga shugaban karamar hukumar, da gwamnatin Jihar Kano da kuma iyalan marigayin bisa mummunan kisan da aka yi wa shugaban al’umma.

A cikin sakon ta’aziyya daban-daban, zababben shugaban kasar ya jajanta wa fitaccen malamin nan Sheikh Ahmad Gumi da ya rasa mahaifiyarsa da kuma iyalan marigayi Janar Sani Abacha bisa rasuwar dansu Abdullahi.

“Akwai kuna rabuwa da masoyi komai yanayi da shekaru.

“Ba za mu iya tambayar Allah ba, sai dai kawai mu yi addu’a Allah Ta’ala ya jikansu, ya kuma ba mu karfin jure wa rashinsu,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya
Manyan Labarai

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa
Manyan Labarai

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Dan Damfara Da Katin Cirar Kudi 10 A Adamawa 

Zaben Gwamnoni: 'Yan Sanda Za Su Hukunta Masu Yada Labaran Karya A Legas

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.