• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin Na Musamman Ya Karyata Zargin Dake Cewa Wai Kasarsa Na Saka Wa Afirka “Tarkon Bashi”

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakilin Sin Na Musamman Ya Karyata Zargin Dake Cewa Wai Kasarsa Na Saka Wa Afirka “Tarkon Bashi”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wakilin musamman a ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin mai kula da yankin kahon Afirka, Xue Bing, ya karyata kalamai marasa tushe dake cewa, wai kasar Sin tana saka wa Afirka “tarkon bashi”.

Xue, ya bayyana a shekaran jiya Talata a Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha, cewa bai dace a dora wa kasar Sin laifin sanya wa Afirka bashi ba.

  • Shanghai Ta Kara Shigar Da Ridi Daga Afirka

Alkaluman da bankin duniya ya fitar a bara sun nuna cewa, daga cikin bashin dala biliyan 696 da ake bin kasashen Afirka 49, kaso 75 bisa dari bashi ne na cibiyoyin hada-hadar kudi na bangarori daban-daban da ’yan kasuwan dake samar da bashi, abun da ya dauki akasarin bashin da ake bin kasashen Afirka. Kana akwai kaso 35 bisa dari na bashin da cibiyoyin samar da bashi masu zaman kansu na kasashen yammacin duniya ke bin kasashen Afirka, adadin da ya ninka kusan sau uku idan aka kwatanta da bashin da kasashen Afirka suka karba daga kasar Sin.

Domin taimakawa kasashen Afirka rage matsin lambar da suke fuskanta a fannin biyan bashi, kasar Sin ta shiga cikin “shawarar dakatar da biyan bashi” da kasashen G20 suka fitar, da rattaba hannu tare da kasashen Afirka 19 kan yarjejeniyar dakatar da biyan bashi, ko kuma cimma matsaya daya kan ragewa ko soke bashi baki daya. Amma akasin haka, wadanda suka fi sauran bangarori bayar da bashi ga kasashen Afirka, ciki har da masu samar da bashi masu zaman kansu na kasa da kasa, da cibiyoyin hada-hadar kudi na bangarori daban-daban, har yanzu ba su dauki matakan ragewa ko kuma soke bashin da suke bin kasashen Afirka ba.

A dayan bangaren kuma, Xue Bing ya ce, kasar Sin na goyon-bayan kasashen yankin kahon Afirka don su warware bambance-bambancen dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, da samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali mai dorewa a wannan yanki.

Labarai Masu Nasaba

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Bugu da kari, a yayin taron manema labarai da aka shirya yau, wani dan jarida ya yi mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin tambayar cewa: Mene ne ra’ayin kasar Sin game da hadin gwiwa tsakanin kasashe da yankin kahon Afirka?

Wang Wenbin ya ba da amsa cewa, a halin yanzu, Habasha na kan wani muhimmin mataki na dawo da zaman lafiya, da mayar da hankali kan bunkasuwa. Mun yi imanin cewa, ya kamata dukkan kasashe su kara yin ayyukan da za su taimaka wajen ci gaban Habasha da samar da zaman lafiya a yankin baki daya, maimakon kakaba takunkumi don tilastawa ko tsoma baki a harkokin cikin gidan wasu kasashe kan wasu batutuwa masu sarkakiya. Kasar Sin tana son yin aiki tare da ragowar kasashen duniya, don taimakawa yankin na Afirka ya zama ginshikin zaman lafiya da hadin gwiwa da samun bunkasuwa cikin hadin gwiwa.

A dangane da batun kare hakkin bil Adama a kasar Amurka kuwa, Wang Wenbin ya ce, abin da ya dace gwamnatin Amurka ta yi shi ne, ta hanzarta magance matsalolin kare hakkin dan-Adam da ke kara ta’azzara a kasarta, kamar nuna wariyar launin fata, laifuffukan kyama, da matsalar harbin bindiga, da laifukan muggan kwayoyi da dai sauransu. (Mai fassarawa: Murtala Zhang, Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Zan Yi Idan Tinubu Ya Ba Ni Mukami A Gwamnatinsa -Peter Obi

Next Post

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Related

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

10 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

14 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

15 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

16 hours ago
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
Daga Birnin Sin

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

17 hours ago
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
Daga Birnin Sin

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

17 hours ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.