• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Atiku Da Obi Sun Shigar Da Kara Ta Kalubalantar Nasarar Tinubu

by Sadiq
3 years ago
Zaben 2023

Jagororin manyan jami’iyyun adawa biyu; PDP da LP, sun shigar da kara a kan neman soke sakamakon zaben shugaban kasa na watan Fabrairu da suke kalubalanta, kamar yadda takardun kotu suka nuna, domin fara wata shari’ar da ka iya daukar tsawon watanni.

An shigar da kararraki da dama na kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar Nijeriya, amma ga dukkan alamu babu wadda ta yi nasara.

  • NIS Reshen Ribas Ta Kafa Kwamitin Bunkasa Walwalar Jami’ai
  • Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

Dan takarar babbar jami’iyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar da Peter Obi na jami’iyar Labour Party, sun roki kotun daukaka kara da ta soke zaben da Bola Tinubu dan takarar jami’iyar APC ya lashe.

Shugabannin jami’iyyun adawan sun fada a wata takardar rantsuwar kotu cewa zaben na tattare da magudi kana sun zargi hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC da take doka, inda ta gaza amfani da na’urar lantarki wajen daukar sakamakon zabe daga runfunan zabe da ma wasu zargi zargin.

Atiku da Obi sun nemi umarnin kotu kan sako bayanan zaben shugaban kasa, kana INEC ta gudanar da sabon zabe.

LABARAI MASU NASABA

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Tinubu ya kare zaben da cewa an gudanar da shi cikin adalci.

Obi da ya shigo takara a karon farko, ya samu goyon bayan matasa da sababbin masu kada kuri’a kuma da alamar ya fadada takarar, inda ya bai wa masu zabe kwarin gwiwar samun sauyi daga shekaru na wahala da tashin hankali karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari mai shekaru 80, tsohon Janar na soja.

Amma Obi ya zo na uku bayan Tinubu da Atiku, wanda dukkaninsu nada jami’iyyu siyasa masu karfi da kuma gomman shekaru na harkokin siyasa.

APC da PDP sune suka gudanar da mulkin Najeriya tsakaninsu tun bayan karshen mulkin soja a shekarar 1999.

Masu sa ido a kan zaben sun zargi INEC da rashin cikakken shiri da kuma jinkiri wurin fara zabe amma basu yi zargin tafka magudi ba. Hukumar kanta ta roki gafara a kan matsalolin na’ura da ta fuskanta wurin kidaya.

Kotun daukaka karar tana da kwanaki 180 ta saurari karar kana ta zartar da hukunci a karar da Obi ya shigar ta kalubalantar sakamakon.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 
Manyan Labarai

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu
Manyan Labarai

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Next Post
Emefiele Ya Roki Gafarar ‘Yan Nijeriya Kan Matsalar Hada-Hadar Kudi Ta Intanet

Emefiele Ya Roki Gafarar 'Yan Nijeriya Kan Matsalar Hada-Hadar Kudi Ta Intanet

LABARAI MASU NASABA

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.