ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Atiku Da Obi Sun Shigar Da Kara Ta Kalubalantar Nasarar Tinubu

by Sadiq
3 years ago
Zaben 2023

Jagororin manyan jami’iyyun adawa biyu; PDP da LP, sun shigar da kara a kan neman soke sakamakon zaben shugaban kasa na watan Fabrairu da suke kalubalanta, kamar yadda takardun kotu suka nuna, domin fara wata shari’ar da ka iya daukar tsawon watanni.

An shigar da kararraki da dama na kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar Nijeriya, amma ga dukkan alamu babu wadda ta yi nasara.

  • NIS Reshen Ribas Ta Kafa Kwamitin Bunkasa Walwalar Jami’ai
  • Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

Dan takarar babbar jami’iyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar da Peter Obi na jami’iyar Labour Party, sun roki kotun daukaka kara da ta soke zaben da Bola Tinubu dan takarar jami’iyar APC ya lashe.

ADVERTISEMENT

Shugabannin jami’iyyun adawan sun fada a wata takardar rantsuwar kotu cewa zaben na tattare da magudi kana sun zargi hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC da take doka, inda ta gaza amfani da na’urar lantarki wajen daukar sakamakon zabe daga runfunan zabe da ma wasu zargi zargin.

Atiku da Obi sun nemi umarnin kotu kan sako bayanan zaben shugaban kasa, kana INEC ta gudanar da sabon zabe.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Tinubu ya kare zaben da cewa an gudanar da shi cikin adalci.

Obi da ya shigo takara a karon farko, ya samu goyon bayan matasa da sababbin masu kada kuri’a kuma da alamar ya fadada takarar, inda ya bai wa masu zabe kwarin gwiwar samun sauyi daga shekaru na wahala da tashin hankali karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari mai shekaru 80, tsohon Janar na soja.

Amma Obi ya zo na uku bayan Tinubu da Atiku, wanda dukkaninsu nada jami’iyyu siyasa masu karfi da kuma gomman shekaru na harkokin siyasa.

APC da PDP sune suka gudanar da mulkin Najeriya tsakaninsu tun bayan karshen mulkin soja a shekarar 1999.

Masu sa ido a kan zaben sun zargi INEC da rashin cikakken shiri da kuma jinkiri wurin fara zabe amma basu yi zargin tafka magudi ba. Hukumar kanta ta roki gafara a kan matsalolin na’ura da ta fuskanta wurin kidaya.

Kotun daukaka karar tana da kwanaki 180 ta saurari karar kana ta zartar da hukunci a karar da Obi ya shigar ta kalubalantar sakamakon.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Emefiele Ya Roki Gafarar ‘Yan Nijeriya Kan Matsalar Hada-Hadar Kudi Ta Intanet

Emefiele Ya Roki Gafarar 'Yan Nijeriya Kan Matsalar Hada-Hadar Kudi Ta Intanet

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.