• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamna Bello Mohammed Matawalle na Jihar Zamfara, ya amince da shan kaye a zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Gwamna mai ci ya sha kaye a hannun dan takarar gwamnan PDP, Dauda Lawal Dare.

  • Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum
  • NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

Gwamnan a wani sakon faifan bidiyo da ya aikewa al’ummar jihar, ya ce dole ne shi da dukkan magoya bayansa su amince da ikon Allah domin al’amura suna faruwa ne kawai da yardarsa, sannan ya yi fatan alheri ga zababben gwamnan yayin da yake tafiyar da harkokin jihar.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa a lokacin da ta fara aiki, ta gana da dukkan manyan masu ruwa da tsaki a jihar kan yadda za su iya kawo zaman lafiya ta hanyar tattaunawar zaman lafiya.

Sai dai ya koka da cewa har zuwa yau babu wani abu da ya fi rashin tsaro da ya janyo asarar rayuka da lalata dukiya.

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Gwamnan ya bayyana cewa baya ga tattaunawar zaman lafiya da ‘yan bindiga, ya yi aiki tukuru don ganin cewa gwamnatinsa ta shigo da bangarori daban-daban na siyasa wuri guda domin samar da zaman lafiya da hadin kai a jihar domin jama’a su rika gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Gwamnan ya ce, “Mun samu sulhu a siyasance kuma hakan ya share fagen yakin neman zabe cikin lumana da kuma harkokin siyasa lafiya a jihar.”

Matawalle ya kuma nemi gafarar duk wanda ya sani ko bai sani ba ya bata masa rai ko ya cutar da su, sannan ya kara da cewa shi mutum ne kamar kowa kuma aikin Allah Madaukakin Sarki ne kadai ba shi da kuskure.

Ya kuma yi kira da a kwantar da hankula tare da tausaya wa wadanda suka yi hasarar dukiya da sunan biki, inda ya jaddada cewa su fahimci cewa ba su da wani wuri sai jihar Zamfara.

Ya kuma yi kira ga gwamnati mai jiran gado da ta zage damtse wajen dawo da zaman lafiya a jihar tare da nuna jin dadin gwamnatin bisa jajircewa da aiki tukuru da jajircewar al’ummar jiharsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.