ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamna Bello Mohammed Matawalle na Jihar Zamfara, ya amince da shan kaye a zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Gwamna mai ci ya sha kaye a hannun dan takarar gwamnan PDP, Dauda Lawal Dare.

  • Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum
  • NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

Gwamnan a wani sakon faifan bidiyo da ya aikewa al’ummar jihar, ya ce dole ne shi da dukkan magoya bayansa su amince da ikon Allah domin al’amura suna faruwa ne kawai da yardarsa, sannan ya yi fatan alheri ga zababben gwamnan yayin da yake tafiyar da harkokin jihar.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa gwamnatinsa a lokacin da ta fara aiki, ta gana da dukkan manyan masu ruwa da tsaki a jihar kan yadda za su iya kawo zaman lafiya ta hanyar tattaunawar zaman lafiya.

Sai dai ya koka da cewa har zuwa yau babu wani abu da ya fi rashin tsaro da ya janyo asarar rayuka da lalata dukiya.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Gwamnan ya bayyana cewa baya ga tattaunawar zaman lafiya da ‘yan bindiga, ya yi aiki tukuru don ganin cewa gwamnatinsa ta shigo da bangarori daban-daban na siyasa wuri guda domin samar da zaman lafiya da hadin kai a jihar domin jama’a su rika gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Gwamnan ya ce, “Mun samu sulhu a siyasance kuma hakan ya share fagen yakin neman zabe cikin lumana da kuma harkokin siyasa lafiya a jihar.”

Matawalle ya kuma nemi gafarar duk wanda ya sani ko bai sani ba ya bata masa rai ko ya cutar da su, sannan ya kara da cewa shi mutum ne kamar kowa kuma aikin Allah Madaukakin Sarki ne kadai ba shi da kuskure.

Ya kuma yi kira da a kwantar da hankula tare da tausaya wa wadanda suka yi hasarar dukiya da sunan biki, inda ya jaddada cewa su fahimci cewa ba su da wani wuri sai jihar Zamfara.

Ya kuma yi kira ga gwamnati mai jiran gado da ta zage damtse wajen dawo da zaman lafiya a jihar tare da nuna jin dadin gwamnatin bisa jajircewa da aiki tukuru da jajircewar al’ummar jiharsu.

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.