ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

by Sadiq
3 years ago
Matawalle

Gwamna Bello Mohammed Matawalle na Jihar Zamfara, ya amince da shan kaye a zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Gwamna mai ci ya sha kaye a hannun dan takarar gwamnan PDP, Dauda Lawal Dare.

  • Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum
  • NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

Gwamnan a wani sakon faifan bidiyo da ya aikewa al’ummar jihar, ya ce dole ne shi da dukkan magoya bayansa su amince da ikon Allah domin al’amura suna faruwa ne kawai da yardarsa, sannan ya yi fatan alheri ga zababben gwamnan yayin da yake tafiyar da harkokin jihar.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa gwamnatinsa a lokacin da ta fara aiki, ta gana da dukkan manyan masu ruwa da tsaki a jihar kan yadda za su iya kawo zaman lafiya ta hanyar tattaunawar zaman lafiya.

Sai dai ya koka da cewa har zuwa yau babu wani abu da ya fi rashin tsaro da ya janyo asarar rayuka da lalata dukiya.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Gwamnan ya bayyana cewa baya ga tattaunawar zaman lafiya da ‘yan bindiga, ya yi aiki tukuru don ganin cewa gwamnatinsa ta shigo da bangarori daban-daban na siyasa wuri guda domin samar da zaman lafiya da hadin kai a jihar domin jama’a su rika gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Gwamnan ya ce, “Mun samu sulhu a siyasance kuma hakan ya share fagen yakin neman zabe cikin lumana da kuma harkokin siyasa lafiya a jihar.”

Matawalle ya kuma nemi gafarar duk wanda ya sani ko bai sani ba ya bata masa rai ko ya cutar da su, sannan ya kara da cewa shi mutum ne kamar kowa kuma aikin Allah Madaukakin Sarki ne kadai ba shi da kuskure.

Ya kuma yi kira da a kwantar da hankula tare da tausaya wa wadanda suka yi hasarar dukiya da sunan biki, inda ya jaddada cewa su fahimci cewa ba su da wani wuri sai jihar Zamfara.

Ya kuma yi kira ga gwamnati mai jiran gado da ta zage damtse wajen dawo da zaman lafiya a jihar tare da nuna jin dadin gwamnatin bisa jajircewa da aiki tukuru da jajircewar al’ummar jiharsu.

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.