• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Da Ke Yi Wa Tumatir Illa Ta Sake Addabar Gonakan Tumatir A Jihar Kano

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Cutar Da Ke Yi Wa Tumatir Illa Ta  Sake Addabar Gonakan Tumatir A Jihar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar manoman Tumatir reshen jihar kano TOGAN ta bayyana cewa, cutar da ke yiwa Tumatir Illa ta sake afkawa a wasu gonakan manona da ke a cikin jihar.

Shugaban kungiyar reshen jihar Alhaji Sani Danladi Yadakwari ne ya bayyana hakan a hirarsa da manema labarai inda ya ce, sun zargin cutar ta Tuta ce da ke lalata Tumatir.

  • Dubi Ga Shirin Nijeriya Na Yaki Da Talauci A Duniya

A cewar shugaban, kungiyar ta dauki kwararan matakai domin mu kare yaduwar cutar zuwa sauran gonakan manoman na Tumatir da ke a daukacin fadin jihar.
Shugaban ya ci gaba da cewa, idan ba yi hankali ba, a kakar noman sa ta bana za a iya samun karancin sa.

” Mun dauki kwararan matakai domin mu kare yaduwar cutar zuwa sauran gonakan manoman na Tumatir da ke a daukacin fadin jihar.”

Yadakwari ya bayyana cewa, mun lura da bullar wannan cutar ta tuta a wasu kananan hukumin Jihar kamar a Garun Mallam da Bunkure da kuma a wasu gurare da ke a cikin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Shugaban ya bayyana cewa, a kungiyance mun yi iya namu kokarin, inda muka rubuta wasiku domin sanar da ma’aikatar aikin noma ta jihar.

Ya sanar da cewa, wannan cutar ba karamar koma baya za ta janyo wa manoman na Tumatir da ke a cikin jihar ba.

Shugaban ya bayyana cewa, ya zama wajibi gwamnatin jihar ta kawo mana daukin gaggawa domin gudun kar manoman na Tumatir da ke a cikin jihar su tabka asara da kuma magance karancin sa a daukacin fadin jihar.

” Ya zama wajibi gwamnatin jihar ta kawo mana daukin gaggawa domin gudun kar manoman na Tumatir da ke a cikin jihar su tabka asara da kuma magance karancin sa a daukacin fadin jihar. ”

Bisa wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, cutar na tafiya ne sai kuma ta sake dawo wa, tum bayan lokacin da ta bulla a shekarar 2016.

” Ya zama wajibi gwamnatin jihar ta kawo mana daukin gaggawa domin gudun kar manoman na Tumatir da ke a cikin jihar su tabka asara da kuma magance karancin sa a daukacin fadin jihar. ”

Da aka tuntubi daraktan ma’aikatar aikin noma da raya karkara na tarayya da ke a cikin jihar Alhaji Baba Gana akan maganar ya bayyana cewa, kungiyar ta tuntubi ma’aikatar kan maganar kuma da zarar sun samu cikakkun bayanai za su dauki matakan da suka kamata akan matsalar, musamman domin a dakile yaduwar cutar zuwa sauran gonakan manoman na noma Tumatir da ke a cikin jihar.

“ Kungiyar ta tuntubi ma’aikatar kan maganar kuma da zarar sun samu cikakkun bayanai za su dauki matakan da suka kamata akan matsalar, musamman domin a dakile yaduwar cutar zuwa sauran gonakan manoman na noma Tumatir da ke a cikin jihar. ”

A wata sabuwa kuwa, wasu daga cikin masana a fannin noman masara a kasar nan, sun sanar da cewa, kokarin manoman ta a kasar nan bai kai ga yanda za’a iya yayatawa ba ba, domin kuwa a ganin su da ace ana aiwatar da abubuwan da ake fada a baki to da yanzu kasar ta tara da takwarorinta da suka yi mata nisa wajen noman rani irin su Masar.

A cewar masanan, Nijeriya za ta iya shiga gaban Masar wajen noman tumatir, saboda idan ka duba , kashi saba’in cikin dari na kasar Masar Sahara ce, inda kuma Nijeriya Allah ya albarkace ta da kasar noma mai inganci, amma bama bin hanyoyin da suka dace.

Masana dai na da ra’ayin cewa da hukumomi a Nijeriya har yanzu ba su fargaba ganin yadda suke yiwa fannin na noma rikon Sakanaira Kashi.

Duk da cewa kasar na daga manyan masu noman tumatur a duniya, har yanzu kasar na shigo da Tumatur daga kasashen waje domin amfanin ‘yan kasar.

Alhaji Abdulrahim Ali wani manomi a karamar hukumar kura a jihar Kano ya sanar da cewa, suna noman tumatir, amma idan masu siya basu zoba, dole ne mu dauka su kai kasuwa mu siyar da araha domin kada ya lallace.

Shi kuwa Malam Dan Lami Umar sakatare na Kungiyar masu sai da kayan gwari ta jihar Kano ya sanar da cewa, wannan shine lokacin da ake asara, saboda ko ta ina akwai kayan miya.

Ya kara da cewa, wani manomin idan kaje gonarsa za ka samu kwando guda dubu biyu zuwa dari biyar ko kuma dari, inda ya kara da cewa, ko kuma idan an kawowa kasuwa, da gwamnatin tana talafawa ba zaa dinga samun irin wannan yanayi ba.

Kwamishinan noma na jihar Kano Alhaji Musa Sulaiman Shanono ya ce gwamnatin ta na iyakacin kokarinta domin magance wanan matsala.

Alhaji Musa ya kara da cewa, gwamnati ta na sane kuma ta damu kwarai, gwamnatin kano ta kulla yarjejeniya domin samarda kamfanin da zai dinga sarrafa tumatir domin taimakawa manoma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Tinubu Ya Kafa Kakkarfar Gwamnati

Next Post

Kano, Borno Da Benuwe Ne A Baya Wajen Bayyana Yadda Suke Kashe Kudadensu – Rahoto

Related

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 days ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

1 week ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

1 week ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

2 weeks ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Kano, Borno Da Benuwe  Ne A Baya Wajen  Bayyana Yadda Suke Kashe Kudadensu – Rahoto

Kano, Borno Da Benuwe Ne A Baya Wajen Bayyana Yadda Suke Kashe Kudadensu - Rahoto

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

June 16, 2025
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Jigila Kai Tsaye Zuwa Sin Da Indiya

FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da KuÉ—in Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa

June 16, 2025
Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

June 16, 2025
Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

June 16, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa ÆŠangote ÆŠanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

June 16, 2025
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

June 16, 2025
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

June 16, 2025
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun Æ™i Amince Wa Da ZaÉ“en Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun Æ™i Amince Wa Da ZaÉ“en Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.