ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dubi Ga Shirin Nijeriya Na Yaki Da Talauci A Duniya

by Bello Hamza
3 years ago
Yaki da talauci

Talauci lamari ne da miliyoyin al’umma ke fuskanta a sassan duniya. Wannan ne babbar dalilin da mutane fiye da 100,000 suka yi gangami a garin Paris ta kasar Faransa a ranar 17 ga watan Oktoba na shekarar 1987 don tattaunawa tare da dubi ga mutanen da ke fama da tsananin talauci a duniya.

Rana ce da aka ware don fadakar da al’umma duniya a kan bukatar samar da hanyoyin kawo kaeshen talauci ta duk hanyar data fito. Rana ce da ake nazari don samar da hanyoyin fitar da dimbin al’ummar da ke fuskantar talauci da dukkan abubuwan da sukan taso sakamakon taualci a cikin al’umma wadanda suka hada da tashe-tashen hankali, cututtuka da rashin muhalli.
Al’umma duniyna amfani da lokacin don karfafa tattauawa da fahimtar juna a tsakanin mutane da rayuwa ke a cikin talauci da kuma al’umma duniya gaba daya.

  • Me Amurka Da Taiwan Suka Yi Kafin Honduras Ta Yanke Hulda Da Taiwan?

Ta nan ne ake samun yanayin tattaunawa da sauraron matane masu fama da talauci don fahimtar cikakken halin da suke ciki tare da tattauna yadda za a tallafa musu.

ADVERTISEMENT

Amma a daidai wannan lokacin mun damu matuka a kan irin barnar da annobar cutar Korona ta yi wanjen kara masu fama da talauci, da tsananin gurbacewar muhalli da kuma abubuwan da yakin Rasha da Yukrain ya haifar wa duniya da kuma yadda lamarin ya haifar da matsananciyar matsalar rashin abinci, a halin yanzu muna fuskantar karanci abinci mafi girma da aka taba fuskanta tun bayan yakin duniya na biyu. Wadannan matsalolin sun kawo cikas ga hanyoyin samar da abinci a wasu lokutta hanyoyin samar da abincin sun kan kulle ne gaba daya, kuma gashi matsaliolin sai kara ta’azzara suke yi, al’umma da dama na cigaba da fuskantar rashin abinci, Talakawa ne suka fi fuskantar wannan matsalar domin kuwa wuraren samun abinci su duk sun bushe a inda kuma ake iya samun abinci yana da tsadar gaske.

A bayyane lamarin yake cewa, al’murra sun rude, iyalai da dama basa iya ciyar da kansu ba wai maganar cin abin mai gida jiki ba, a ma dai samu abinci da za a ci. Abin da ke faruwa sakamakon rashin cin abinci mai gina jiki shi ne cutar yunwa da cututtuka masu tsanani a cikin al’umma, wannan kuma ya fi tsanani ne a tsakanin yara kanana don kuwa karancin abinci ya zamma wani makami da ke cutar da yaran talakawa.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Yawan ‘yan Nijeriya da ke fuskantar matsalar rashin abinci mai gina jiki da za su ci da rashin kayan sawa da kuma matsugunai yana karuwa ne a kullum garin Allah ya waye. Wannan abin talaici ne in aka lura da dimbin albarkatun kasa da Allah ya hore mana wannan sai dai ace babu cikkakiyar damuwa ne da rashin sanin yakamata.

Abin kura a kan lamarin talaucin da ake fuskantar Nijeriya shi ne na yadda a duk shedkara ake jin gwamnati na ware dimbin kudade da sunan yaki da talauci amma kuma al’amarin a kullum sai kara kazancewa yake yi.

Wannan Jaridar ta lura da cewa, duk ikirarin da wannan gwamnatin ke yi na cewa ta fitar da al’ummar Nijeriya fiye da Miliyan 100 daga kangin talauci a cikin shekara 10 amma har yanzu Nijeriya na nan rike da kambunta na hedikwatar talauci na duniya, inda ake da fiye da mutum miliyan 93.9 da ke rayuwa a cikin talauci.

Amma dai gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, shirin nan na fitar da mutum miliyan 100 daga kangin talauci zai tabbata ne daga shekarar 2030, inhar dukkan masu truwa da tsaki suka bayar da nasu gudummawar yadda yakamata. Wannan dai da kamar wuya, in har gwamnati ta kasa yakar cinhaci da rashawa wadda ke ta kara ta’azzara a kullum.

A shekarar 2019, gwamnatin tarayya ta yi watsi da wani rahoto inda aka ayyana Nijeriya a matsayin hedikwatar talauci a duniya duk kuwa da shugabannin duniya kamar Firayministan Birtaniya Theresa May, ta kara jaddada wannan matsayar. Daga baya an bayyana mana cewa, Shugaba Buhari zai mayar da hankali a yaki da talauci a zangonsa na biyu a ofis.

Amma a yanzu kusan saura wata 7 zuwa karshen wa’adinsa na biyuu amma babu wata kwakwarar hujja da ke nuna cewa, abubuwa sun inganta a kan yadda suke a shekarar 2019.

Maimakon haka ma al’ummura sun kara tabarbarewa ne, tun daga lamarin tsaro ga shi kuma matsalar ambaliyar ruwa da ta addabi sassan kasar nan na cigaba da wahalar da al’umma.

Tabbas za a iya magance talauci, ba bin da ba zai iya yiwuwa ba ne. daya daga cikin hanyoyin magance talaucin shi ne sanya talakawa a cikin tattauanwar fito da hanyoyin magance talaucin da kuma karfafa tattalin arziki da samar da hanyoyin aikin yi ga al’ummar Nijeriya, haka kuma dole a yi maganin banbancin da ake nunawa a tsakanin jinsin maza da mata, yana kuma matukar muhimmanci a inganta cibiyoyin al’umma, wannan tabbas zai matukar kawa karshen talauci a tsakanin al’ummar duniya gaba daya.

Muna kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da sanya tsare-tsaren yaki da talauci a cikin tsarin ayyyukanta tare da kuma tabbatar da ana aiwatar da tsarin ba tare da bata lokaci ba, ta haka ‘yan Nijeriya da dama za su samu fita daga kangin talauci.

Haka kuma yakamata gwammati ta zuba jari a harkokin kasuwanci a yankunan karkara wanda ta haka al’umma gaba daya za su amfana

Yaki da talauci
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Wakilin Sin Ya Jaddada Matsayin Nahiyar Afirka Na Kasancewa A Kan Gaba Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Tsaron Kanta

Wakilin Sin Ya Jaddada Matsayin Nahiyar Afirka Na Kasancewa A Kan Gaba Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Tsaron Kanta

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.