• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Makoma Mai Haske Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A baya bayan nan, hukumar lafiya ta duniya WHO ta bayyana raguwar adadin masu harbuwa da cutar COVID-19 a nahiyar Afirka da kaso mai yawa, tun daga tsakiyar watan Afirilun da ya gabata, raguwar da a cewar hukumar ita ce mafi tsawo da aka samu a nahiyar tun bullar wannan annoba kawo yanzu.

Ko shakka babu wannan labari ne mai faranta rai ga duniya baki daya. To sai dai kuma, wani jan aiki dake gaban kasashen nahiyar ta Afirka a yanzu shi ne lalubo hanyoyin shawo kan mummunan tasirin da wannan annoba ta haifar musamman ta fuskar tattalin arzikin Afirka.

  • Sin Tana Adawa Da Dokar Hana Kayayyakin Da Suka Shafi Jihar Xinjiang Shiga Amurka

Hakan ne ma ya sa masharhanta da dama ke ganin ya zama wajibi kasashen Afirka su karfafa hadin gwiwarsu da kasar Sin, karkashin muhimman manufofin hadin kai da sassan biyu suka jima da amincewa da su, wadanda suka hada da manufofin da aka tsara karkashin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, da ayyukan samar da moriya dake kunshe cikin shawarar nan ta ziri daya da hanya daya da sauran su.

A halin da ake ciki, kasar Sin ce babbar abokiyar huldar nahiyar Afirka ta fuskar kasuwanci cikin sama da shekaru 10, kuma kasar da kamfanoninta ke kara zuba jari mai yawan gaske a nahiyar, wanda adadinsa ya karu a watanni 7 na farkon shekarar 2021 zuwa dalar Amurka biliyan 2.07.

A bangaren nahiyar Afirka, masana na cewa, nahiya ce dake da tarin albarkatun kasa, da maadanai masu daraja, da man fetur da iskar gas, da damar samar da makamashi daga hasken rana, da fadin kasar noma mai yalwa, da tarin alumma dake cikin shekarun kwadago.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sai dai kuma kalubalen rashin masanaantu, da kamfar makamashi, ya zamowa nahiyar kadangaren bakin tulu, ta yadda kasashen nahiyar ba sa samun damar cin gajiyar da ta dace daga albarkatunta. Hakan ya sa kasashen Afirka da dama kasancewa cikin jerin kasashe mafiya fama da talauci a duniya.

Duk da wadannan tarin kalubale, akwai makoma mai haske ga kasashen na Afirka, muddin sun ci gaba da nacewa aiwatar da kudurorin dake kunshe cikin ajandojin wanzar da ci gaban su, tare da babbar manufar nan ta raya hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka ta nan da shekarar 2035, ko China-Africa Cooperation Vision 2035 a Turance, da ma shirin dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da Afirka na Dakar, mai kunshe da tsarin ayyuka da za a aiwatar tsakanin shekarar nan ta 2022 zuwa 2024.

Dukkanin wadannan kudurori ne da ke kunshe cikin babbar manufar nan ta shawarar ziri daya da hanya daya da kasar Sin ta gabatarwa duniya, wadda ko shakka babu, ci gaba da aiwatar da ita zai haifarwa kasashen na Afirka tarin alfanu nan da shekaru masu zuwa. (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika
Daga Birnin Sin

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Next Post
Yadda Wani Lauya Ya Tarwatsa Dakin Shari’a Da Shigar Matsubbata

Yadda Wani Lauya Ya Tarwatsa Dakin Shari'a Da Shigar Matsubbata

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.